< Numbers 2 >
1 And the Lord spoke to Moses and Aaron, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
2 All the children of Israel shall camp by their troops, ensigns, and standards, and the houses of their kindreds, round about the tabernacle of the covenant.
“Duk sa’ad da Isra’ilawa suka yi sansani, kowane mutum zai sauka a inda tutar ƙungiyar kabilarsa take. Sansanin zai kasance a kewaye da Tentin Sujada.”
3 On the east Juda shall pitch his tents by the bands of his army: and the prince of his sons shall be Nahasson the son of Aminadab.
Kabilar Yahuda za su yi sansani bisa ga ƙa’idarsu a gabas, wajen fitowar rana. Shugaban mutanen Yahuda kuwa shi ne Nashon ɗan Amminadab.
4 And the whole sum of the fighting men of his stock, were seventy-four thousand six hundred.
Yawan mutanen sashensa 74,600 ne.
5 Next unto him they of the tribe of Issachar encamped, whose prince was Nathanael, the son of Suar.
Kabilar Issakar za su yi sansani biye da su. Shugabansu shi ne Netanel ɗan Zuwar.
6 And the whole number of his fighting men were fifty-four thousand four hundred.
Yawan mutanen sashensa 54,400 ne.
7 In the tribe of Zabulon the prince was Eliab the son of Helon.
Kabilar Zebulun za su yi sansani biye da su. Shugabansu shi ne Eliyab ɗan Helon.
8 And all the army of fighting men of his stock, were fifty-seven thousand four hundred.
Yawan mutanen sashensa 57,400 ne.
9 All that were numbered in the camp of Juda, were a hundred and eighty-six thousand four hundred: and they by their troops shall march first.
Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Yahuda bisa ga sashensu sun kai 186,400. Su ne za su ja gaba.
10 In the camp of the sons of Ruben, on the south side, the prince shall be Elisur the son of Sedeur:
A kudu, a nan ne sashe sansanin mutanen Ruben a ƙarƙashin ƙa’idarsu, za su yi sansani. Shugaban mutanen Ruben shi ne Elizur ɗan Shedeyur.
11 And the whole army of his fighting men, that were numbered, were forty-six thousand five hundred.
Yawan mutanen sashensa 46,500 ne.
12 Beside him camped they of the tribe of Simeon: whose prince was Salamiel the son of Surisaddai.
Kabilar Simeyon za su yi sansani biye da su. Shugaban mutanensa shi ne Shelumiyel ɗan Zurishaddai.
13 And the whole army of his fighting men, that were numbered, were fifty-nine thousand three hundred.
Yawan mutanen sashensa 59,300 ne.
14 In the tribe of Gad the prince was Eliasaph the son of Duel.
Kabilar Gad za su zama na biye. Shugaban mutanensa shi ne Eliyasaf ɗan Reyuwel.
15 And the whole army of his fighting men that were numbered, were forty-five thousand six hundred and fifty.
Yawan mutanen sashensa 45,650 ne.
16 All that were reckoned up in the camp of Ruben, were a hundred and fifty-one thousand four hundred and fifty, by their troops: they shall march in the second place.
Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Ruben, bisa ga sashensu sun kai 151,450. Su ne za su zama na biyu in za a tashi.
17 And the tabernacle of the testimony shall be carried by the officers of the Levites and their troops. As it shall be set up, so shall it be taken down. Every one shall march according to their places, and ranks.
Sa’an nan Lawiyawa ɗauke da Tentin Sujada za su kasance a tsakiyar sansani sa’ad da aka tashi tafiya. Za su kama hanya kamar yadda aka dokace su su zauna a sansani, kowa a wurinsa a ƙarƙashin ƙa’idarsu.
18 On the west side shall be the camp of the sons of Ephraim, whose prince was Elisama, the son of Ammiud.
Ta wajen yamma kuma sashen Efraim za su yi sansani a ƙarƙashin ƙa’idarsu. Shugaban mutanensa, shi ne Elishama ɗan Ammihud.
19 The whole army of his fighting men, that were numbered, were forty thousand five hundred.
Yawan mutanen sashensa 40,500 ne.
20 And with them the tribe of the sons of Manasses, whose prince was Gamaliel the son of Phadassur.
Kabilar Manasse ce za tă zama ta biye. Shugabansu shi ne Gamaliyel ɗan Fedazur.
21 And the whole army of his fighting men, that were numbered, were thirty-two thousand two hundred.
Yawan mutanen sashensa 32,200 ne.
22 In the tribe of the sons of Benjamin the prince was Abidan the son of Gedeon.
Na biye da su su ne mutanen Benyamin. Shugaban mutanensu kuwa Abidan ɗan Gideyoni.
23 And the whole army of his fighting men, that were reckoned up, were thirty-five thousand four hundred.
Yawan mutanen sashensa 35,400 ne.
24 All that were numbered in the camp of Ephraim, were a hundred and eight thousand one hundred by their troops: they shall march in the third place.
Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Efraim, bisa ga sashensu su kai 108,100 ne. Su ne za su zama na uku sa’ad da za a tashi.
25 On the north side camped the sons of Dan: whose prince was Ahiezar the son of Ammisaddai.
A arewa za a sami sashen sansanin Dan, a ƙarƙashin ƙa’idarsu. Shugabansu shi ne Ahiyezer ɗan Ammishaddai.
26 The whole army of his fighting men, that were numbered, were sixty-two thousand seven hundred.
Yawan mutanen sashensa 62,700 ne.
27 Beside him they of the tribe of Aser pitched their tents: whose prince was Phegiel the son of Ochran.
Kabilar Asher ce za tă zama ta biye. Shugabansu shi ne Fagiyel ɗan Okran.
28 The whole army of his fighting men, that were numbered, were forty-one thousand five hundred.
Yawan mutanen sashensa 41,500 ne.
29 Of the tribe of the sons of Nephtali the prince was Ahira the son of Enan.
Kabilar Naftali za su zama na biye da su. Shugaban mutanen kuwa shi ne Ahira ɗan Enan.
30 The whole army of his fighting men, were fifty-three thousand four hundred.
Yawan mutanen sashensa 53,400 ne
31 All that were numbered in the camp of Dan, were a hundred and fifty-seven thousand six hundred: and they shall march last.
Dukan mazan da aka ba su aiki a sansanin Efraim, bisa ga sashensu su kai 157,600. Su ne za su zama na ƙarshe, ƙarƙashin ƙa’idarsu.
32 This is the number of the children of Israel, of their army divided according to the houses of their kindreds and their troops, six hundred and three thousand five hundred and fifty.
Waɗannan su ne Isra’ilawan da aka a ƙidaya bisa ga iyalansu. Dukansu da suke a sansani, mutane 603,550 ne.
33 And the Levites were not numbered among the children of Israel: for so the Lord had commanded Moses.
Ba a dai ƙidaya Lawiyawa tare da sauran Isra’ilawa ba yadda Ubangiji ya umarci Musa.
34 And the children of Israel did according to all things that the Lord had commanded. They camped by their troops, and marched by the families and houses of their fathers.
Saboda haka Isra’ilawa suka yi duk ko mene ne da Ubangiji ya umarci Musa. Ta haka ne suka yi sansani a ƙarƙashin ƙa’idarsu kowanne tare da kabilarsa da danginsa.