< Nehemiah 11 >

1 And the princes of the people dwelt at Jerusalem: but the rest of the people cast lots, to take one part in ten to dwell in Jerusalem the holy city, and nine parts in the other cities.
To, fa, shugabannin mutane suka zauna a Urushalima, sauran mutanen kuma suka jefa ƙuri’a don su kawo mutum ɗaya daga kowane mutum goma don su zauna a Urushalima, birni mai tsarki, yayinda sauran tara suka zauna a garuruwansu.
2 And the people blessed all the men that willingly offered themselves to dwell in Jerusalem.
Sai mutane suka yaba wa dukan mutanen da suka ba da kansu da yardar rai su zauna a Urushalima.
3 These therefore are the chief men of the province, who dwelt in Jerusalem, and in the cities of Juda. And every one dwelt in his possession, in their cities: Israel, the priests, the Levites, the Nathinites, and the children of the servants of Solomon.
Waɗannan su ne shugabannin yankuna waɗanda suka zauna a Urushalima (ko da yake waɗansu Isra’ilawa, da firistoci, da Lawiyawa, da ma’aikatan haikali, da zuriyar bayin Solomon, suka yi zama a cikin garuruwan Yahuda, kowanne a mallakarsa cikin garuruwa dabam-dabam,
4 And in Jerusalem there dwelt some of the children of Juda, and some of the children of Benjamin: of the children of Juda, Athaias the son of Aziam, the son of Zacharias, the son of Amarias, the son of Saphatias, the son of Malaleel: of the sons of Phares,
yayinda sauran mutane daga Yahuda da Benyamin suka zauna a Urushalima). Daga zuriyar Yahuda akwai, Atahiya ɗan Uzziya, ɗan Zakariya, ɗan Amariya, ɗan Shefatiya, ɗan Mahalalel, wani zuriyar Ferez;
5 Maasia the son of Baruch, the son of Cholhoza, the son of Hazia, the son of Adaia, the son of Joiarib, the son of Zacharias, the son of the Silonite:
da Ma’asehiya ɗan Baruk, ɗan Kol-Hoze, ɗan Hazahiya, ɗan Adahiya, ɗan Yohiyarib, ɗan Zakariya, zuriyar Shela.
6 All these the sons of Phares, who dwelt in Jerusalem, were four hundred sixty-eight valiant men.
Zuriyar Ferez waɗanda suka zauna a Urushalima sun kai ɗari huɗu da sittin da takwas, dukansu kuwa muhimman mutane ne.
7 And these are the children of Benjamin: Sellum the son of Mosollam, the son of Joed, the son of Phadaia, the son of Colaia, the son of Masia, the son of Etheel, the son of Isaia.
Daga zuriyar Benyamin akwai, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Yowed, ɗan Fedahiya, ɗan Kolahiya, ɗan Ma’asehiya, ɗan Itiyel, ɗan Yeshahiya,
8 And after him Gebbai, Sellai, nine hundred twenty-eight.
da mabiyansa, Gabbai da Sallai, mutum 928.
9 And Joel the son of Zechri their ruler, and Judas the son of Senua was second over the city.
Yowel ɗan Zikri ne babban shugabansu, Yahuda kuma ɗan Hassenuwa, ya shugabanci Yanki na Biyu na birni.
10 And of the priests Idaia the son of Joarib, Jachin,
Daga firistoci akwai, Yedahiya ɗan Yohiyarib, da Yakin,
11 Saraia the son of Helcias, the son of Mosollam, the son of Sadoc, the son of Meraioth, the son of Achitob the prince of the house of God,
da Serahiya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, mai lura da abubuwa a cikin gidan Allah,
12 And their brethren that do the works of the temple: eight hundred twenty-two. And Adaia the son of Jeroham, the son of Phelelia, the son of Amsi, the son of Zacharias, the son of Pheshur, the son of Melchias,
tare da’yan’uwansu waɗanda suke aiki domin haikali, su 822 ne. Akwai kuma Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Felaliya, ɗan Amzi, ɗan Zakariya, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya,
13 And his brethren the chiefs of the fathers: two hundred forty-two. And Amassai the son of Azreel, the son of Ahazi, the son of Mosollamoth, the son of Emmer,
da’yan’uwansa waɗanda suke shugabannin iyalai, su 242. Sai kuma Amashsai ɗan Azarel, ɗan Ahzai, ɗan Meshillemot, ɗan Immer,
14 And their brethren who were very mighty, a hundred twenty-eight: and their ruler Zabdiel son of the mighty.
da’yan’uwansa, su 128 ne muhimman mutane. Babban shugabansu shi ne Zabdiyel ɗan Haggedolim.
15 And of the Levites Semeia the son of Hasub, the son of Azaricam, the son of Hasabia, the son of Boni,
Daga Lawiyawa kuwa akwai, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, ɗan Bunni,
16 And Sabathai and Jozabed, who were over all the outward business of the house of God, of the princes of the Levites,
da Shabbetai, da kuma Yozabad, biyu cikin shugabanni Lawiyawa waɗanda suke da nawayar aiki waje da gidan Allah.
17 And Mathania the son of Micha, the son of Zebedei, the son of Asaph, was the principal man to praise, and to give glory in prayer, and Becbecia the second, one of his brethren, and Abda the son of Samua, the son of Galal, the son of Idithun.
Sai kuma Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zabdi, ɗan Asaf, shugaban da yake bi da hidimar godiya da kuma addu’a. Sai Bakbukiya, na biyu a cikin’yan’uwansa; da Abda ɗan Shammuwa, ɗan Galal, ɗan Yedutun.
18 All the Levites in the holy city were two hundred eighty-four.
Lawiyawan da suke cikin birni mai tsarki sun kai 284.
19 And the porters, Accub, Telmon, and their brethren, who kept the doors: a hundred seventy-two.
Matsaran ƙofofi kuwa su ne, Akkub, da Talmon, da’yan’uwansu waɗanda suke tsaron ƙofofi, su 172 ne.
20 And the rest of Israel, the priests and the Levites were in all the cities of Juda, every man in his possession.
Sauran Isra’ilawa tare da firistoci, da Lawiyawa sun kasance a dukan garuruwan Yahuda, kowanne a mallakar kakansa.
21 And the Nathinites, that dwelt in Ophel, and Siaha, and Gaspha of the Nathinites.
Ma’aikatan haikali sun zauna a kan tudun Ofel. Ziha, da Gishfa ne suke lura da su.
22 And the overseer of the Levites in Jerusalem, was Azzi the son of Bani, the son of Hasabia, the son of Mathania, the son of Micha. Of the sons of Asaph, were the singing men in the ministry of the house of God.
Babban shugaban Lawiyawa a Urushalima shi ne Uzzi ɗan Bani, ɗan Hashabiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mika. Uzzi yana ɗaya daga zuriyar Asaf, waɗanda suke mawaƙan da suke da nawayar hidima a gidan Allah.
23 For the king’s commandment was concerning them, and an order among the singing men day by day.
Mawaƙa sun bi umarnan sarki, a kan abin da za su yi kowace rana.
24 And Phathahia the son of Mesezebel of the children of Zara the son of Juda was at the hand of the king, in all matters concerning the people,
Fetahahiya ɗan Meshezabel, ɗaya daga zuriyar Zera ɗan Yahuda ne, wakilin sarki cikin dukan al’amuran da suka shafi mutane.
25 And in the houses through all their countries. Of the children of Juda so dwelt at Cariath-Arbe, and in the villages thereof: and at Dibon, and in the villages thereof: and at Cabseel, and in the villages thereof.
Game da ƙauyukan da filayensu, waɗansu mutanen Yahuda suka zauna a Kiriyat Arba da ƙauyukanta, da Dibon da ƙauyukanta, da Yekabzeyel da ƙauyukanta.
26 And at Jesue, and at Molada, and Bethphaleth,
Akwai su kuma a Yeshuwa, da Molada, da Bet-Felet,
27 And at Hasersual, and at Bersabee, and in the villages thereof,
da Hazar Shuwal, da Beyersheba da ƙauyukanta.
28 And at Siceleg, and at Mochona, and in the villages thereof,
Akwai su a Ziklag, da Mekona da ƙauyukanta.
29 And at Remmon, and at Saraa, and at Jerimuth,
Suna nan kuma a En Rimmon, da Zora, da Yarmut,
30 Zanoa, Odollam, and in their villages, at Lachis and its dependencies, and at Azeca and the villages thereof. And they dwelt from Bersabee unto the valley of Ennom.
da Zanowa, da Adullam da ƙauyukansu, da Lakish da gonakinta, da kuma Azeka da ƙauyukanta. Saboda haka sun yi zama tun daga Beyersheba har zuwa Kwarin Hinnom.
31 And the children of Benjamin, from Geba, at Mechmas, and at Hai, and at Bethel, and in the villages thereof,
Zuriyar mutanen Benyamin daga Geba sun zauna a Mikmash, da Aiya, da Betel da ƙauyukanta,
32 At Anathoth, Nob, Anania,
da Anatot, da Nob, da Ananiya,
33 Asor, Rama, Gethaim,
da Hazor, da Rama, da Gittayim,
34 Hadid, Seboim, and Neballat, Led,
da Hadid, da Zeboyim, da Neballat,
35 And Ono the valley of craftsmen.
da Lod, da Ono, da kuma a Kwarin Masu sana’a.
36 And of the Levites were portions of Juda and Benjamin.
Waɗansu gundumomin Lawiyawan Yahuda sun zauna a Benyamin.

< Nehemiah 11 >