< Nehemiah 10 >

1 And the subscribers were Nehemias, Athersatha the son of Hachelai, and Sedecias,
Waɗanda suka buga hatimin su ne, Nehemiya ɗan Hakaliya, wanda yake gwamna. Zedekiya
2 Saraias, Azarias, Jeremias,
da Serahiya, da Azariya, da Irmiya,
3 Pheshur, Amarias, Melchias,
da Fashhur, da Amariya, da Malkiya,
4 Hattus, Sebenia, Melluch,
da Hattush, da Shebaniya, da Malluk,
5 Harem, Merimuth, Obdias,
da Harim, da Meremot, da Obadiya,
6 Daniel, Genthon, Baruch,
da Daniyel, da Ginneton, da Baruk,
7 Mosollam, Abia, Miamin,
da Meshullam, da Abiya, da Miyamin,
8 Maazia, Belgia, Semeia: these were priests.
da Ma’aziya, da Bilgai, da kuma Shemahiya. Waɗannan su ne Firistocin.
9 And the Levites, Josue the son of Azanias, Bennui of the sons of Henadad. Cedmihel,
Lawiyawan kuwa su ne, Yeshuwa ɗan Azaniya, da Binnuyi ɗan Henadad, da Kadmiyel,
10 And their brethren, Sebenia, Oduia, Celita, Phalaia, Hanan,
’yan’uwansu kuwa su ne, Shebaniya, da Hodiya, da Kelita, da Felahiya, da Hanan,
11 Micha, Rohob, Hasebia,
da Mika, da Rehob, da Hashabiya,
12 Zachur, Serebia, Sabania,
da Zakkur, da Sherebiya, da Shebaniya,
13 Odaia, Bani, Baninu.
da Hodiya, da Bani da kuma Beninu.
14 The heads of the people, Pharos, Phahath Moab, Elam, Zethu, Bani,
Shugabannin mutane su ne, Farosh, da Fahat-Mowab, da Elam, da Zattu, da Bani,
15 Bonni, Azgad, Bebai,
da Bunni, da Azgad, da Bebai,
16 Adonia, Begoai, Adin,
da Adoniya, da Bigwai, da Adin,
17 Ater, Hezecia, Azur,
da Ater, da Hezekiya, da Azzur,
18 Odaia, Hasum, Besai,
da Hodiya, da Hashum, da Bezai,
19 Hareph, Anathoth, Nebai,
da Harif, da Anatot, da Nebai,
20 Megphias, Mosollam, Hazir,
da Magfiyash, da Meshullam, da Hezir,
21 Mesizabel, Sadoc, Jeddua,
da Meshezabel, da Zadok, da Yadduwa
22 Pheltia, Hanan, Anaia,
da Felatiya, da Hanan, da Anahiya,
23 Osee, Hanania, Hasub,
da Hosheya, da Hananiya, da Hasshub,
24 Alohes, Phalea, Sobec,
da Hallohesh, da Filha, da Shobek,
25 Rehum, Hasebna, Maasia,
da Rehum, da Hashabna, da Ma’asehiya
26 Echaia, Hanan, Anan,
da Ahiya, da Hanan, da Anan,
27 Melluch, Haran, Baana:
da Malluk, da Harim da kuma Ba’ana.
28 And the rest of the people, priests, Levites, porters, and singing men, Nathinites, and all that had separated themselves from the people of the lands to the law of God, their wives, their sons, and their daughters.
“Sauran mutane, wato, firistoci, Lawiyawa, matsaran ƙofofi, mawaƙa, ma’aikatan haikali da dukan waɗanda suka ware kansu daga maƙwabta saboda Dokar Allah, tare da matansu da dukan’ya’yansu maza da mata waɗanda za su iya fahimta,
29 All that could understand promising for their brethren, with their chief men, and they came to promise, and swear that they would walk in the law of God, which he gave in the hand of Moses the servant of God, that they would do and keep all the commandments of the Lord our God, and his judgments and his ceremonies.
dukan waɗannan yanzu suka sadu da manyan gari’yan’uwansu, suka rantse, cewa la’ana ta same su idan ba su kiyaye Dokar Allah da aka bayar ta wurin Musa bawan Allah su kuma mai da hankali ga yin biyayya da dukan umarnai, ƙa’idodi da farillan Ubangiji shugabanmu ba.
30 And that we would not give our daughters to the people of the land, not take their daughters for our sons.
“Mun yi alkawari ba za mu ba da’ya’yanmu mata aure ga mutanen da suke kewaye da mu ba, ba kuwa za mu auri’ya’yansu mata wa’ya’yanmu maza ba.
31 And if the people of the land bring in things to sell, or any things for use, to sell them on the sabbath day, that we would not buy them of them on the sabbath, or on the holy day. And that we would leave the seventh year, and the exaction of every hand.
“Sa’ad da maƙwabta suka kawo kayayyaki ko hatsi don su sayar a ranar Asabbaci, ba za mu saya daga gare su a ranar Asabbaci ko a rana mai tsarki ba. Kowace shekarar Asabbaci ba za mu nome ƙasa ba kuma za mu yafe kowane irin bashi.
32 And we made ordinances for ourselves, to give the third part of a side every year for the work of the house of our God,
“Mun ɗauka hakkin bin umarnai na ba da kashi ɗaya bisa uku na shekel kowace shekara don hidimar gidan Allahnmu.
33 For the leaves of proposition, and for the continual sacrifice, and for a continual holocaust on the sabbaths, on the new moons, on the set feasts, and for the holy things, and for the sin offering: that atonement might be made for Israel, and for every use of the house of our God.
Za mu tanada burodin da ake ajiye a kan tebur; za mu ba da hadayun hatsi da hadayun ƙonawa na kullum; za mu ba da hadayun Asabbatai, da na bukukkuwan Sabon Wata da na bukukkuwan da aka ƙayyade; za mu ba da hadayu masu tsarki; za mu ba da hadayun zunubi don a yi kafara domin Isra’ila; mu kuma ba da abubuwan da ake bukata dukan domin ayyukan gidan Allahnmu.
34 And we cast lots among the priests, and the Levites, and the people for the offering of wood, that it might be brought into the house of our God by the houses of our fathers at set times, from year to year: to burn upon the altar of the Lord our God, as it is written in the law of Moses:
“Mu, firistoci, da Lawiyawa da kuma mutane, mun jefa ƙuri’a don a san lokacin da kowane iyalinmu zai kawo sadakar itace don ƙonewa a gidan Allahnmu a ƙayyadaddun lokuta a bagaden Ubangiji Allahnmu, kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka.
35 And that we would bring the first fruits of our land, and the firstfruits of all fruit of every tree, from year to year, in the house of our Lord.
“Mun kuma ɗauka hakkin kawo nunan fari na hatsinmu da kuma na kowane itace mai ba da’ya’ya a gidan Ubangiji kowace shekara.
36 And the firstborn of our sons, and of our cattle, as it is written in the law, and the firstlings of our oxen, and of our sheep, to be offered in the house of our God, to the priests who minister in the house of our God.
“Kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka, za mu kawo ɗan fari na’ya’yanmu maza da na garken shanunmu, da na tumakinmu, da kuma na awakinmu a gidan Allahnmu, don firistocin da suke aikin a can.
37 And that we would bring the firstfruits of our meats, and of our libations, and the fruit of every tree, of the vintage also and of oil to the priests, to the storehouse of our God, and the tithes of our ground to the Levites. The Levites also shall receive the tithes of our works out of all the cities.
“Ban da haka ma, za mu kawo wa ɗakunan ajiyar gidan Allahnmu, abincinmu na farko daga ƙasa, na hadayun hatsinmu, na’ya’yan dukan itatuwanmu da kuma na sabon ruwan inabinmu da mai namu wa firistoci. Za mu kuma kawo zakkar hatsinmu wa Lawiyawa, gama Lawiyawa ne ke karɓan Zakka cikin dukan garuruwan da muke noma.
38 And the priest the son of Aaron shall be with the Levites in the tithes of the Levites, and the Levites shall offer the tithe of their tithes in the house of our God, to the storeroom into the treasure house.
Firist wanda yake daga zuriyar Haruna zai raka Lawiyawa sa’ad da suke karɓan zakka, Lawiyawan kuma za su kawo kashi ɗaya bisa goma na zakka zuwa gidan Allahnmu, su kawo a ɗakunan ajiya na baitulmali.
39 For the children of Israel and the children of Levi shall carry to the treasury the firstfruits of corn, of wine, and of oil: and the sanctified vessels shall be there, and the priests, and the singing men, and the porters, and ministers, and we will not forsake the house of our God.
Mutanen Isra’ila haɗe da Lawiyawa, za su kawo sadakokinsu na hatsi, sabon ruwan inabi da mai a ɗakunan ajiya inda ake ajiyar kayayyakin wuri mai tsarki da kuma inda firistoci, matsaran ƙofofi da kuma mawaƙa suke zama. “Ba za mu ƙyale gidan Allahnmu ba.”

< Nehemiah 10 >