< Matthew 27 >

1 And when morning was come, all the chief priests and ancients of the people took counsel against Jesus, that they might put him to death.
Da gari ya waye, duk manyan firistoci da dattawan jama'a suka shirya yadda zasu kulla makirci domin su kashe shi.
2 And they brought him bound, and delivered him to Pontius Pilate the governor.
Suka daure shi, suka mika shi ga gwamna Bilatus.
3 Then Judas, who betrayed him, seeing that he was condemned, repenting himself, brought back the thirty pieces of silver to the chief priests and ancients,
Sa'adda Yahuza, wanda ya bashe shi, ya ga an zartarwa Yesu hukuncin kisa, ya nemi tuba ya kuma mayar da azurfar talatin ga manyan firistocin da dattawan,
4 Saying: I have sinned in betraying innocent blood. But they said: What is that to us? look thou to it.
yace, “Na yi zunubi ta wurin cin amanar mara laifi.” Amma sukace, “Ina ruwan mu? Ka ji da shi da kanka?”
5 And casting down the pieces of silver in the temple, he departed: and went and hanged himself with an halter.
Sai ya jefar da kwandalolin azurfar a kasa cikin haikalin ya kuma bar su, ya tafi ya rataye kansa.
6 But the chief priests having taken the pieces of silver, said: It is not lawful to put them into the corbona, because it is the price of blood.
Sai babban firist ya dauki kwandalolin azurfar ya ce, “Ba daidai bane bisa ga shari'a musa wannan cikin ma'aji, saboda kudin jini ne.”
7 And after they had consulted together, they bought with them the potter’s field, to be a burying place for strangers.
Sai suka tattauna al'amarin a tsakanin su, kudin kuma suka sayi filin maginin tukwane domin makabatar baki.
8 For this cause the field was called Haceldama, that is, The field of blood, even to this day.
Dalilin wannan ne ake kiran wurin, “Filin jini” har yau.
9 Then was fulfilled that which was spoken by Jeremias the prophet, saying: And they took the thirty pieces of silver, the price of him that was prized, whom they prized of the children of Israel.
Sai abin da aka fada ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa, “Suka dauki tsabar azurfa talatin na farashin da mutanen Isra'ila suka sa a kansa,
10 And they gave them unto the potter’s field, as the Lord appointed to me.
suka bayar domin sayen filin mai tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”
11 And Jesus stood before the governor, and the governor asked him, saying: Art thou the king of the Jews? Jesus saith to him: Thou sayest it.
Sai Yesu ya tsaya a gaban gwamna, gwamna ya kuma tambaye shi, “Kai sarkin Yahudawa ne?” Yesu ya amsa, “Haka ka fada.”
12 And when he was accused by the chief priests and ancients, he answered nothing.
Amma da manyan firistocin da dattawan suka zarge shi, bai ce komai ba.
13 Then Pilate saith to him: Dost not thou hear how great testimonies they allege against thee?
Sai Bilatus yace masa, “Baka ji dukan zarge-zargen da ake yi maka ba?”
14 And he answered him to never a word; so that the governor wondered exceedingly.
Amma bai ce masa ko kalma guda ba, sai gwamna yayi matukar mamaki.
15 Now upon the solemn day the governor was accustomed to release to the people one prisoner, whom they would.
To lokacin bikin idi, al'adar gwamna ne ya saki mutum guda wanda jama'a suka zaba.
16 And he had then a notorious prisoner, that was called Barabbas.
A wannan lokacin suna da wani sanannen dan kurkuku mai suna Barabbas.
17 They therefore being gathered together, Pilate said: Whom will you that I release to you, Barabbas, or Jesus that is called Christ?
To da suka tattaru, sai Bilatus yace masu, “Wa kuke so a sakar maku? Barabbas, ko Yesu wanda ake kira Almasihu?”
18 For he knew that for envy they had delivered him.
Saboda ya san sun kawo shi ne domin kishi.
19 And as he was sitting in the place of judgment, his wife sent to him, saying: Have thou nothing to do with that just man; for I have suffered many things this day in a dream because of him.
Da yake zaune a kujerar shari'a, matarsa ta aika masa cewa, “Ka fita sha'anin mutumin nan marar laifi. Saboda na sha wahala sosai a yau cikin mafarki saboda shi.”
20 But the chief priests and ancients persuaded the people, that they should ask Barabbas, and make Jesus away.
A lokacin nan manyan firistoci da dattawa suka rinjayi ra'ayin jama'a suce a sakar masu da Barabbas, a kashe Yesu.
21 And the governor answering, said to them: Whether will you of the two to be released unto you? But they said, Barabbas.
Sai gwamna ya tambayesu, “Wa kuke so a sakar maku?” Sukace, “Barabbas.”
22 Pilate saith to them: What shall I do then with Jesus that is called Christ? They say all: Let him be crucified.
Bilatus yace masu, “Me zan yi da Yesu wanda ake kira Almasihu?” Sai duka suka amsa, “A gicciye shi.”
23 The governor said to them: Why, what evil hath he done? But they cried out the more, saying: Let him be crucified.
Sai yace, “Don me, wane laifi ya aikata?” Amma suka amsa da babbar murya, “A gicciye shi”
24 And Pilate seeing that he prevailed nothing, but that rather a tumult was made; taking water washed his hands before the people, saying: I am innocent of the blood of this just man; look you to it.
Amma da Bilatus ya ga ba zai iya komai ba don hargitsi zai iya barkewa, ya dauki ruwa ya wanke hannuwansa a gaban jama'a, yace, “Ba ni da laifi ga jinin mutumin nan marar laifi. Ku yi abin da kuka ga dama.”
25 And the whole people answering, said: His blood be upon us and our children.
Duka mutanen sukace, “Bari jininsa ya kasance a kan mu da 'ya'yan mu.”
26 Then he released to them Barabbas, and having scourged Jesus, delivered him unto them to be crucified.
Sai ya sakar masu da Barabbas amma yayi wa Yesu bulala ya mika shi garesu domin su gicciye shi.
27 Then the soldiers of the governor taking Jesus into the hall, gathered together unto him the whole band;
Sai sojojin gwamna suka dauki Yesu zuwa farfajiya suka kuma tara dukan rundunar sojoji.
28 And stripping him, they put a scarlet cloak about him.
Suka yi masa tumbur sa'annan suka sa masa jar alkyabba.
29 And platting a crown of thorns, they put it upon his head, and a reed in his right hand. And bowing the knee before him, they mocked him, saying: Hail, king of the Jews.
Sai suka yi masa rawanin kaya suka sa a kansa, suka kuma bashi sanda a hannunsa na dama. Suka rusuna a gabansa suna masa ba'a, suna cewa, “Ranka ya dade, Sarkin Yahudawa!”
30 And spitting upon him, they took the reed, and struck his head.
Suka kuma tofa masa yawu, suka kwace sandar suka buga masa a ka.
31 And after they had mocked him, they took off the cloak from him, and put on him his own garments, and led him away to crucify him.
Bayan sun gama masa ba'a, suka cire masa alkyabbar suka sa masa kayansa, suka jagorance shi zuwa wurin da za a gicciye shi.
32 And going out, they found a man of Cyrene, named Simon: him they forced to take up his cross.
Da suka fito waje, sai suka iske wani Bakurame mai suna Saminu, wanda suka tilasta ya tafi tare dasu domin ya dauki gicciyen.
33 And they came to the place that is called Golgotha, which is the place of Calvary.
Suka iso wani wuri da ake kira Golgotta, wanda ke nufin,”Wurin kwalluwa.”
34 And they gave him wine to drink mingled with gall. And when he had tasted, he would not drink.
Suka bashi ruwan inabi da aka gauraya da wani abu mai daci. Amma da ya 'dan-'dana shi sai ya ki sha.
35 And after they had crucified him, they divided his garments, casting lots; that it might be fulfilled which was spoken by the prophet, saying: They divided my garments among them; and upon my vesture they cast lots.
Bayan da suka gicciye shi, suka kada kuri'a a kan rigarsa.
36 And they sat and watched him.
Suka kuma zauna suna kallonsa.
37 And they put over his head his cause written: THIS IS JESUS THE KING OF THE JEWS.
A sama da kansa suka sa abinda ake tuhumarsa da ita a rubuce, “Wannan shine sarkin Yahudawa.”
38 Then were crucified with him two thieves: one on the right hand, and one on the left.
An gicciye shi da 'yanfashi guda biyu, daya ta damansa dayan kuma ta hagunsa.
39 And they that passed by, blasphemed him, wagging their heads,
Wadanda suke wucewa suna zaginsa, suna girgiza kai,
40 And saying: Vah, thou that destroyest the temple of God, and in three days dost rebuild it: save thy own self: if thou be the Son of God, come down from the cross.
suna kuma cewa, “Kai da kace zaka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku, ka ceci kanka mana! In dai kai Dan Allah ne, ka sauko daga gicciyen!”
41 In like manner also the chief priests, with the scribes and ancients, mocking, said:
Ta haka ma manyan firistocin suka rika yi masa ba'a, tare da marubuta da shugabannin, suna cewa,
42 He saved others; himself he cannot save. If he be the king of Israel, let him now come down from the cross, and we will believe him.
“Ya ceci wasu amma ya kasa ceton kansa. Shi ne sarkin Isra'ila. Ya sauko mana daga kan gicciyen, sai mu ba da gaskiya gareshi.
43 He trusted in God; let him now deliver him if he will have him; for he said: I am the Son of God.
Tun da ya yarda da Allah. Bari Allahn ya cece shi mana, saboda yace, “Ni dan Allah ne.”
44 And the selfsame thing the thieves also, that were crucified with him, reproached him with.
Hakan nan ma 'yanfashin guda biyu da aka gicciye su tare suka zage shi.
45 Now from the sixth hour there was darkness over the whole earth, until the ninth hour.
To tun da tsakar rana sai duhu ya rufe kasar gaba daya har karfe uku na yamma.
46 And about the ninth hour Jesus cried with a loud voice, saying: Eli, Eli, lamma sabacthani? that is, My God, my God, why hast thou forsaken me?
Wajen karfe uku, Yesu ya tada murya mai karfi yace, “Eli, Eli lama sabaktani?” wanda ke nufin, “Allahna, Allahna, don me ka yashe ni?”
47 And some that stood there and heard, said: This man calleth Elias.
Da wadanda suke tsaye kusa suka ji haka, sai sukace, “Yana kiran Iliya.”
48 And immediately one of them running took a sponge, and filled it with vinegar; and put it on a reed, and gave him to drink.
Nan take wani ya ruga da gudu ya dauki soso ya tsoma cikin ruwan inabi mai tsami ya soka kan sandar kara ya mika masa ya sha.
49 And the others said: Let be, let us see whether Elias will come to deliver him.
Sai sauran sukace, “Rabu da shi mu gani ko Iliya zai zo ya cece shi.”
50 And Jesus again crying with a loud voice, yielded up the ghost.
Sai Yesu ya ta da murya mai karfi yayi kuka sai ya saki ruhunsa.
51 And behold the veil of the temple was rent in two from the top even to the bottom, and the earth quaked, and the rocks were rent.
Sai labullen haikali ya yage gida biyu daga sama zuwa kasa. Kasa kuma ta girgiza, duwatsu suka farfashe.
52 And the graves were opened: and many bodies of the saints that had slept arose,
Kaburbura suka bude, tsarkaka kuwa wadanda suke barci da yawa suka tashi.
53 And coming out of the tombs after his resurrection, came into the holy city, and appeared to many.
Suka fito daga kaburbura bayan tashinsa, suka shiga birni mai tsarki suka bayyana ga mutane da yawa.
54 Now the centurion and they that were with him watching Jesus, having seen the earthquake, and the things that were done, were sore afraid, saying: Indeed this was the Son of God.
Da hafsan sojan da wadanda suke kallon Yesu suka ga girgizar kasar da abinda ya faru, suka ji tsoro kwarai sukace, “Hakika wannan Dan Allah ne”
55 And there were there many women afar off, who had followed Jesus from Galilee, ministering unto him:
Mata dayawa da suka bi Yesu daga Galili domin su lura da shi suka tsaya suna kallo daga nesa.
56 Among whom was Mary Magdalen, and Mary the mother of James and Joseph, and the mother of the sons of Zebedee.
A cikin su akwai Maryamu Magadaliya, Maryamu uwar Yesu da Yusufu, da uwar 'ya'yan Zabadi.
57 And when it was evening, there came a certain rich man of Arimathea, named Joseph, who also himself was a disciple of Jesus.
Da yamma sai wani attajiri mutumin Armatiya ya zo, mai suna Yusufu wanda shi ma almajirin Yesu ne.
58 He went to Pilate, and asked the body of Jesus. Then Pilate commanded that the body should be delivered.
Ya je wurin Bilatus ya roka a bashi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a bashi.
59 And Joseph taking the body, wrapped it up in a clean linen cloth.
Yusufu ya dauki jikin, ya rufe shi da likafani mai tsabta,
60 And laid it in his own new monument, which he had hewed out in a rock. And he rolled a great stone to the door of the monument, and went his way.
sai ya sa shi a cikin sabon kabarinsa da ya sassaka cikin dutse. Sai ya mirgina babban dutse a bakin kofar kabarin ya tafi.
61 And there was there Mary Magdalen, and the other Mary sitting over against the sepulchre.
Maryamu Magadaliya da dayan Maryamun suna nan zaune akasin kabarin.
62 And the next day, which followed the day of preparation, the chief priests and the Pharisees came together to Pilate,
Washegari, wato bayan ranar Shiri, Sai manyan firistoci da Farisawa suka taru tare da Bilatus.
63 Saying: Sir, we have remembered, that that seducer said, while he was yet alive: After three days I will rise again.
Sukace, “Mai gida, mun tuna lokacin da mayaudarin nan yake da rai, yace, “Bayan kwana uku zan tashi.”
64 Command therefore the sepulchre to be guarded until the third day: lest perhaps his disciples come and steal him away, and say to the people: He is risen from the dead; and the last error shall be worse than the first.
Saboda haka, ka bada umarni a tsare kabarin na kwana uku. In ba haka ba almajiransa zasu zo su sace shi, kuma su ce wa mutane, “Ya tashi daga mattatu.” Kuma yaudarar karshe zata fi ta farko muni.”
65 Pilate saith to them: You have a guard; go, guard it as you know.
Bilatus yace masu, “Ku dauki masu tsaro. Kuyi tsaro iyakar karfin ku.”
66 And they departing, made the sepulchre sure, sealing the stone, and setting guards.
Sai suka tafi suka tsare kabarin, suka hatimce dutsen, suka sa masu tsaro.

< Matthew 27 >