< Matthew 24 >
1 And Jesus being come out of the temple, went away. And his disciples came to shew him the buildings of the temple.
Yesu ya fita daga cikin haikalin ya kama hanyar sa. Almajiran sa suka zo suna nuna masa ginin haikali.
2 And he answering, said to them: Do you see all these things? Amen I say to you there shall not be left here a stone upon a stone that shall not be destroyed.
Amma ya amsa masu yace, “kun ga dukkan wadannan abubuwan? Ina gaya maku gaskiya, ba ko dutse daya da za'a bari akan dan'uwansa wanda ba za'a rushe shi ba.”
3 And when he was sitting on mount Olivet, the disciples came to him privately, saying: Tell us when shall these things be? and what shall be the sign of thy coming, and of the consummation of the world? (aiōn )
Yayin da ya zauna a kan dutsen zaitun, almajiran sa suka zo wurin sa a boye suka ce, “me zai zama alamar zuwanka da kuma na karshen duniya?” (aiōn )
4 And Jesus answering, said to them: Take heed that no man seduce you:
Yesu ya amsa yace dasu, “Ku kula kada wani yasa ku kauce.”
5 For many will come in my name saying, I am Christ: and they will seduce many.
Gama da yawa za su zo da sunana. Za su ce, “ni ne almasihu,” kuma za su sa da yawa su kauce.
6 And you shall hear of wars and rumours of wars. See that ye be not troubled. For these things must come to pass, but the end is not yet.
Za ku ji labarin yake-yake da kuma shelar yake-yake. Ku kula kar ku tsorata, domin dole abubuwan nan su faru; amma karshen dai tukunna.
7 For nation shall rise against nation, and kingdom against kingdom; and there shall be pestilences, and famines, and earthquakes in places:
Gama al'umma zata tayarwa al'umma, kuma mulki zai tayarwa mulki. Za'a yi yunwa da girgizar kasa a wurare dabam dabam.
8 Now all these are the beginnings of sorrows.
Amma dukkan wadannan farkon ciwon haihuwa ne kawai.
9 Then shall they deliver you up to be afflicted, and shall put you to death: and you shall be hated by all nations for my name’s sake.
Bayan haka za'a bada ku ga tsanani a kuma kashe ku. Dukkan al'ummai za su tsane ku saboda sunana.
10 And then shall many be scandalized: and shall betray one another: and shall hate one another.
Daga nan da yawa za su yi tuntube, kuma su ci amanar juna, su kuma tsani juna.
11 And many false prophets shall rise, and shall seduce many.
Annabawan karya da yawa za su taso kuma susa da yawa su kauce.
12 And because iniquity hath abounded, the charity of many shall grow cold.
Domin mugunta zata ribambanya, kaunar masu yawa zata yi sanyi.
13 But he that shall persevere to the end, he shall be saved.
Amma duk wanda ya jure har karshe, zai sami ceto.
14 And this gospel of the kingdom, shall be preached in the whole world, for a testimony to all nations, and then shall the consummation come.
Za'a yi wa'azin wannan bisharar mulkin a dukkan duniya don ya zama shaida akan dukkan al'ummai. Daganan karshen zai zo.
15 When therefore you shall see the abomination of desolation, which was spoken of by Daniel the prophet, standing in the holy place: he that readeth let him understand.
Don haka, idan kun ga abin kyama mai lalatarwa, wanda Annabi Daniyel ya yi maganar sa, Ya tsaya a wuri mai tsarki (bari mai karatu ya fahimta),
16 Then they that are in Judea, let them flee to the mountains:
bari wadanda ke yahudiya su gudu zuwa kan duwatsu,
17 And he that is on the housetop, let him not come down to take any thing out of his house:
Bari wanda yake kan bene kada ya sauko don daukar wani abu a cikin gidansa,
18 And he that is in the field, let him not go back to take his coat.
kuma wanda yake gona kar ya dawo gida domin daukar babbar rigarsa.
19 And woe to them that are with child, and that give suck in those days.
Amma kaito ga wadanda suke dauke da yaro, ko masu shayarwa a wannan kwanakin!
20 But pray that your flight be not in the winter, or on the sabbath.
Ku yi addu'a kada gudun ku ya zama lokacin hunturu, ko ranan asabaci.
21 For there shall be then great tribulation, such as hath not been from the beginning of the world until now, neither shall be.
Domin za'ayi tsanani mai girma, wanda ba'a taba yin irin shi ba, tun farkon duniya har ya zuwa yau, a'a ba za ayi irin shi ba kuma.
22 And unless those days had been shortened, no flesh should be saved: but for the sake of the elect those days shall be shortened.
In ba don an rage kwanakin ba, da ba mahalukin da zai tsira. Amma albarkacin zababbun, za a rage kwanakin.
23 Then if any man shall say to you: Lo here is Christ, or there, do not believe him.
Sa'annan idan wani yace maku, duba, “ga Almasihu a nan!” ko, “ga Almasihu a can!” kar ku gaskata.
24 For there shall arise false Christs and false prophets, and shall show great signs and wonders, insomuch as to deceive (if possible) even the elect.
Gama annabawan karya da almasihan karya za su zo suna nuna alamu da al'ajibai, don su yaudari masu yawa zuwa ga bata, in ya yiwuma har da zababbun.
25 Behold I have told it to you, beforehand.
Kun gani, na gaya maku kafin lokacin ya zo.
26 If therefore they shall say to you: Behold he is in the desert, go ye not out: Behold he is in the closets, believe it not.
Saboda haka, idan suka ce maku, “ga shi a jeji,” kar ku je jejin. Ko, “ga shi a can cikin kuryar daki,” kar ku gaskata.
27 For as lightning cometh out of the east, and appeareth even into the west: so shall the coming of the Son of man be.
Yadda walkiya ke haskakawa daga gabas zuwa yamma, haka nan zuwan Dan mutum zai zama.
28 Wheresoever the body shall be, there shall the eagles also be gathered together.
Duk inda mushe yake, nan ungulai suke taruwa.
29 And immediately after the tribulation of those days, the sun shall be darkened and the moon shall not give her light, and the stars shall fall from heaven, and the powers of heaven shall be moved:
Amma nan da nan bayan kwanakin tsananin nan, rana za ta duhunta, wata kuma ba zai ba da haskensa ba, taurari kuma za su fado daga sama, ikokin sammai za su girgiza.
30 And then shall appear the sign of the Son of man in heaven: and then shall all tribes of the earth mourn: and they shall see the Son of man coming in the clouds of heaven with much power and majesty.
Sa'annan alamar Dan Mutum za ta bayyana a sararin sama, kuma dukkan kabilun duniya za su yi bakin ciki. Za su ga Dan Mutun na zuwa a gajimarai da iko da daukaka mai girma.
31 And he shall send his angels with a trumpet, and a great voice: and they shall gather together his elect from the four winds, from the farthest parts of the heavens to the utmost bounds of them.
Zai aiki mala'ikunsa, da karar kaho mai karfi, kuma za su tattara dukkan zababbu daga dukkan kusurwoyi hudu, daga karshen sararin sama har zuwa wani karshen.
32 And from the fig tree learn a parable: When the branch thereof is now tender, and the leaves come forth, you know that summer is nigh.
Kuyi koyi da itacen baure. Da zaran reshen sa ya yi toho ya fara bada ganye, za ku sani bazara ta kusa.
33 So you also, when you shall see all these things, know ye that it is nigh, even at the doors.
Haka kuma, idan kun ga dukkan wadannan abubuwa, ya kamata ku sani, Ya yi kusa, ya na bakin kofa.
34 Amen I say to you, that this generation shall not pass, till all these things be done.
Ina gaya maku gaskiya, wannan zamanin ba zai wuce ba, sai dukkan wadannan abubuwan sun faru.
35 Heaven and earth shall pass, but my words shall not pass.
Sama da kasa za su shude, amma kalmomina ba za su shude ba.
36 But of that day and hour no one knoweth, not the angels of heaven, but the Father alone.
Amma game da ranan nan ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai Uban kadai.
37 And as in the days of Noe, so shall also the coming of the Son of man be.
Kamar yadda kwanakin Nuhu suke, haka zai zama game da zuwan Dan Mutum.
38 For as in the days before the flood, they were eating and drinking, marrying and giving in marriage, even till that day in which Noe entered into the ark,
A wadannan kwankin kafin zuwan ruwan tsufana suna ci suna sha, suna aure suna aurarwa har ranar da Nuhu ya shiga jirgin,
39 And they knew not till the flood came, and took them all away; so also shall the coming of the Son of man be.
ba su san kome ba har ruwan ya zo ya cinye su haka ma zuwan Dan Mutun zai zama.
40 Then two shall be in the field: one shall be taken, and one shall be left.
Sa'annan mutane biyu zasu kasance a gona za a dauke daya, a bar daya a baya.
41 Two women shall be grinding at the mill: one shall be taken, and one shall be left.
Mata biyu na nika a manika za a dauke daya, za a bar dayar.
42 Watch ye therefore, because ye know not what hour your Lord will come.
Don haka sai ku yi zaman tsaro, domin baku san ranar da Ubangijinku zai zo ba.
43 But know this ye, that if the goodman of the house knew at what hour the thief would come, he would certainly watch, and would not suffer his house to be broken open.
Amma ku san wannan, idan maigida ya san lokacin da barawo zai zo, zai zauna a shirye ba zai bar gidan sa har a balle a shiga ba.
44 Wherefore be you also ready, because at what hour you know not the Son of man will come.
Don haka sai ku shirya, domin Dan Mutum zai zo a sa'ar da ba ku yi zato ba.
45 Who, thinkest thou, is a faithful and wise servant, whom his lord hath appointed over his family, to give them meat in season.
To wanene amintaccen bawannan mai hikima, wanda maigidan sa ya sa ya kula mar da gida, domin ya ba su abinci a kan lokaci?
46 Blessed is that servant, whom when his lord shall come he shall find so doing.
Mai albarka ne bawan, da mai gidan zai same shi a kan aikin sa a lokacin da ya dawo.
47 Amen I say to you, he shall place him over all his goods.
Ina gaya maku gaskiya mai gidan zai dora shi a kan dukkan a binda yake da shi.
48 But if that evil servant shall say in his heart: My lord is long a coming:
Amma idan mugun bawa ya ce a zuciyarsa, “maigida na ya yi jinkiri,”
49 And shall begin to strike his fellow servants, and shall eat and drink with drunkards:
sai ya fara dukan sauran barorin, ya yi ta ci da sha tare da mashaya,
50 The lord of that servant shall come in a day that he hopeth not, and at an hour that he knoweth not:
uban gidan bawan zai dawo a ranar da bawan bai zata ba, a lokacin da bai sani ba.
51 And shall separate him, and appoint his portion with the hypocrites. There shall be weeping and gnashing of teeth.
Uban gidansa zai datsa shi biyu, karshen sa zai zama daidai da na munafukai, za a sashi inda a ke kuka da cizon hakora.