< Mark 12 >

1 And he began to speak to them in parables: A certain man planted a vineyard and made a hedge about it, and dug a place for the winefat, and built a tower, and let it to husbandmen; and went into a far country.
Sai Yesu ya fara koyar da su da misalai. “Wani mutum ne ya yi gonar inabi ya shingen ta, ya haka ramin matse inabin, ya kuwa gina hasumayar tsaro. Ya ba wandansu manoma jinginar gonar, sa'an nan ya tafi wata kasa mai nisa.
2 And at the season he sent to the husbandmen a servant to receive of the husbandmen of the fruit of the vineyard.
Da lokaci ya yi, sai ya aika masu wani bawansa domin ya karbi wadansu daga cikin amfanin gonar.
3 Who having laid hands on him, beat him, and sent him away empty.
Amma manoman suka kama shi, suka yin masa duka, suka kore shi hannu banza.
4 And again he sent to them another servant; and him they wounded in the head, and used him reproachfully.
Ya sake aikar wani bawan. Shi kuma suka raunata shi aka, suka wulakanta shi.
5 And again he sent another, and him they killed: and many others, of whom some they beat, and others they killed.
Ya sake aiken wani. Shi kam, suka kashe shi. Haka fa aka yi ta yi da wadansu da yawa, sun dodoki wadansu, suka kuma kashe wadansu.
6 Therefore having yet one son, most dear to him; he also sent him unto them last of all, saying: They will reverence my son.
Yanzu dai yana da sauran daya tak, shine kaunatacen dansa. Daga karshe ya aike shi wurinsu, yana cewa, ai za su bashi girma.
7 But the husbandmen said one to another: This is the heir; come let us kill him; and the inheritance shall be ours.
Amma manoman nan suka ce wa juna, “ai, wannan shine magajinsa, 'ku zo mu kashe shi, gadon ya zama namu.”
8 And laying hold on him, they killed him, and cast him out of the vineyard.
Sai suka kamo shi, suka kashe shi, suka jefar da shi bayan shinge.
9 What therefore will the lord of the vineyard do? He will come and destroy those husbandmen; and will give the vineyard to others.
To, me mai gonar inabin zai yi? Sai ya zo ya hallaka manoman nan, ya ba wadansu gonar.
10 And have you not read this scripture, The stone which the builders rejected, the same is made the head of the corner:
Ashe, ba ku karanta wannan nassi ba? cewa, ' Dutsen da magina suka ki, shi ne ya zama mafi mahmimanci.
11 By the Lord has this been done, and it is wonderful in our eyes.
Wannan daga Ubangiji ne, kuma ya yi dai dai a idanunmu.”'
12 And they sought to lay hands on him, but they feared the people. For they knew that he spoke this parable to them. And leaving him, they went their way.
Sai suka nemi su kama shi, don sun lura a kansu ne ya yi masalin, amma suka ji tsoron jama'a. Don haka suka kyele shi, suka tafi.
13 And they sent to him some of the Pharisees and of the Herodians; that they should catch him in his words.
Suka aika masa da wadansu farisiyawa da Heridiyawa, don su sa masa tarko da kalamai cikin maganarsa.
14 Who coming, say to him: Master, we know that thou art a true speaker, and carest not for any man; for thou regardest not the person of men, but teachest the way of God in truth. Is it lawful to give tribute to Caesar; or shall we not give it?
Da suka zo, suka ce masa, “Malam, gaskiya kana koyar da maganar Allah sosai, ba ka nuna bambanci tsakani mutane, sai koyar da tafarkin Allah kake yi sosai. “Shin, mu biya haraji ga Kaisar, ko a a?”
15 Who knowing their wiliness, saith to them: Why tempt you me? bring me a penny that I may see it.
AmmaYesu ya gane munafuncinsu, ya ce masu, “Don me kuke gwada ni? ku kawo mani dinarin in gani.”
16 And they brought it him. And he saith to them: Whose is this image and inscription? They say to him, Caesar’s.
Suka kawowa Yesu daya. Ya ce masu, “Kamar waye da kuma rubutun wanene? suka ce masa, “Na Kaisar ne.”
17 And Jesus answering, said to them: Render therefore to Caesar the things that are Caesar’s, and to God the things that are God’s. And they marvelled at him.
Yesu ya ce, “to, ku ba Kaisar abinda yake na Kaisar, ku kuma ba Allah abin da yake na Allah. Sai suka yi mamakinsa kwarai.
18 And there came to him the Sadducees, who say there is no resurrection; and they asked him, saying:
Sai Sadukiyawa suka zo wurinsa, su dake cewa babu tashin matattu. Suka tambaya shi suka ce,
19 Master, Moses wrote unto us, that if any man’s brother die, and leave his wife behind him, and leave no children, his brother should take his wife, and raise up seed to his brother.
“Malam, Musa dai ya rubuta mana, cewa idan dan'uwan mutum ya mutu, ya bar matarsa ba da, lallai ne dan'uwan mutumin ya auri matar, ya haifa wa dan'uwansa 'ya'ya.'
20 Now there were seven brethren; and the first took a wife, and died leaving no issue.
To an yi wadansu 'yan'uwa maza guda bakwai, na farko ya yi aure, ya mutu bai bar 'ya'ya ba.
21 And the second took her, and died: and neither did he leave any issue. And the third in like manner.
Na biyu kuma ya aure ta, shi ma ya mutu, ba 'ya'ya. Na ukun ma haka.
22 And the seven all took her in like manner; and did not leave issue. Last of all the woman also died.
Haka dai duk bakwai din, ba wanda ya bar 'ya'ya. A karshe kuma ita matar ta mutu.
23 In the resurrection therefore, when they shall rise again, whose wife shall she be of them? for the seven had her to wife.
To, a tashin matattu, matar wa za ta zama a cikinsu? Don duk bakwai din nan sun aure ta”.
24 And Jesus answering, saith to them: Do ye not therefore err, because you know not the scriptures, nor the power of God?
Sai Yesu ya ce, “Ba saboda wannan dalili ne kuka yi kuskure ba, wato don ba ku san littafin ba, kuma ba ku san ikon Allah ba?
25 For when they shall rise again from the dead, they shall neither marry, nor be married, but are as the angels in heaven.
Domin in an tashin daga matattu, ba a aure, ba a auraswa, amma sun zama kamar malaiku a sama.
26 And as concerning the dead that they rise again, have you not read in the book of Moses, how in the bush God spoke to him, saying: I am the God of Abraham, and the God of Isaac, and the God of Jacob?
Amma game da mattattun da suka tashi, ashe, ba ku taba karantawa a littafin Musa ba, yadda Allah ya ce masa? “Ni ne Allah na Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu'?
27 He is not the God of the dead, but of the living. You therefore do greatly err.
Ai, shi ba Allahn mattatu bane, amma na rayyayu ne. Hakika kun yi kuskure “.
28 And there came one of the scribes that had heard them reasoning together, and seeing that he had answered them well, asked him which was the first commandment of all.
Sai wani malamin attuara ya zo ya ji suna muhawara da juna. Da dai ya ga Yesu yana ba su kyakkyawar amsa, sai ya tambaye shi, “Wanne Umarni ne mafi girma dukka?”
29 And Jesus answered him: The first commandment of all is, Hear, O Israel: the Lord thy God is one God.
Yesu ya amsa yace, “mafi girma shine, 'ku saurara ya Isra'ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji daya ne.
30 And thou shalt love the Lord thy God, with thy whole heart, and with thy whole soul, and with thy whole mind, and with thy whole strength. This is the first commandment.
Sai ka kaunaci Ubangiji Allah da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka da dukkan tunaninka, da dukkan karfinka.
31 And the second is like to it: Thou shalt love thy neighbour as thyself. There is no other commandment greater than these.
ta biyu itace, 'ka kaunaci makwabcinka kamar kanka, Ba wata doka da ta fi wadannan.''
32 And the scribe said to him: Well, Master, thou hast said in truth, that there is one God, and there is no other besides him.
Sai malamin attaura ya ce masa, “Hakika gaskiyarka malam, Allah daya ne, ba kuma wani sai shi.
33 And that he should be loved with the whole heart, and with the whole understanding, and with the whole soul, and with the whole strength; and to love one’s neighbour as one’s self, is a greater thing than all holocausts and sacrifices.
A kaunace shi kuma da dukkan zuciya, da dukkan hankali, da dukkan karfi, a kuma kaunaci makwabci kamar kanka, ai ya fi dukkan hadayu na konawa.”
34 And Jesus seeing that he had answered wisely, said to him: Thou art not far from the kingdom of God. And no man after that durst ask him any question.
Da Yesu ya ga ya yi masa magana da hikima, sai ya ce masa, “Ba ka nesa da mulkin Allah.” Bayan wannan kuma ba wanda ya sake tambayarsa wani abu.
35 And Jesus answering, said, teaching in the temple: How do the scribes say, that Christ is the son of David?
Yesu ya amsa a lokacin da yake koyarwa a Haikali, ya ce “Yaya malaman attaura suke ce wa Kristi dan Dauda ne?
36 For David himself saith by the Holy Ghost: The Lord said to my Lord, Sit on my right hand, until I make thy enemies thy footstool.
Domin Dauda kansa, ta ikon Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Ubangiji ya ce wa Ubangijina, zauna a hannun damana, har sai na kaskantar da makiyanka'.
37 David therefore himself calleth him Lord, and whence is he then his son? And a great multitude heard him gladly.
Dauda da kansa ya kira shi 'Ubangiji; To, ta yaya ya Almasihu zai zama Dan Dauda?” Babban taron jama'ar suka saurare shi da murna.
38 And he said to them in his doctrine: Beware of the scribes, who love to walk in long robes, and to be saluted in the marketplace,
A koyarwa sa Yasu ya ce, “ku yi hankali da malaman attaura, masu son yawo da manyan riguna, suna so a gaishesu a kasuwa,
39 And to sit in the first chairs, in the synagogues, and to have the highest places at suppers:
da kuma son wuraren zama masu daraja a haikali, da wurin bukukuwa.
40 Who devour the houses of widows under the pretence of long prayer: these shall receive greater judgment.
Sun kuma kwace gidajen gwauraye, da yin doguwar addu'a, don mutane su gani. Wadanan mutanen zasu sami hukunci mai tsanani.”
41 And Jesus sitting over against the treasury, beheld how the people cast money into the treasury, and many that were rich cast in much.
Sai ya zauna a gaban akwatin baiko a Haikalin, yana duban yadda jama'a suke zuba kudi a ciki.
42 And there came a certain poor widow, and she cast in two mites, which make a farthing.
Wadansu masu arziki da yawa suna zuba kudi masu tsoka. Sai gwauruwa mara abin hanu ta saka anini biyu a ciki akwatin baikon.
43 And calling his disciples together, he saith to them: Amen I say to you, this poor widow hath cast in more than all they who have cast into the treasury.
Ya kira almajiransa, ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, abinda gwauruwa nan ta saka a akwatin baikon nan ya fi na sauran dukka.
44 For all they did cast in of their abundance; but she of her want cast in all she had, even her whole living.
Su duk sun bayar daga yalwa tasu ne, ita kuwa daga cikin rashinta ta bada duk abinda take da shi.”

< Mark 12 >