< Luke 20 >

1 And it came to pass, that on one of the days, as he was teaching the people in the temple, and preaching the gospel, the chief priests and the scribes, with the ancients, met together,
Ana nan wata rana, Yesu yana kan koyarwa a haikali da wa'azin bishara, sai shugaban firistoci da marubuta suka zo wurinsa da dattawa.
2 And spoke to him, saying: Tell us, by what authority dost thou these things? or, Who is he that hath given thee this authority?
Suka yi magana, su na ce masa, “Gaya mana da wanne iko ne ka ke yin wadannan abubuwan? Ko wanene ya baka wannan ikon?”
3 And Jesus answering, said to them: I will also ask you one thing. Answer me:
Ya amsa sai ya ce masu, “Ni ma zan yi maku tambaya. Gaya mani game
4 The baptism of John, was it from heaven, or of men?
da baptisman Yahaya. Daga sama take ko kuwa daga mutane ne?”
5 But they thought within themselves, saying: If we shall say, From heaven: he will say: Why then did you not believe him?
Sai suka yi mahawara da junansu, suna cewa, “In mun ce, 'Daga sama,' zai ce, 'To don me ba ku ba da gaskiya gareshi ba?'
6 But if we say, Of men, the whole people will stone us: for they are persuaded that John was a prophet.
Amma in mun ce, 'Daga mutane ne,' dukan mutane za su jejjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata a ransu Yahaya annabi ne.”
7 And they answered, that they knew not whence it was.
Sai suka amsa cewa ba su san ko daga ina ne take ba.
8 And Jesus said to them: Neither do I tell thee by what authority I do these things.
Yesu yace masu, “To haka ni ma ba zan gaya maku ko da wanne iko nake yin wadannan abubuwan ba.”
9 And he began to speak to the people this parable: A certain man planted a vineyard, and let it out to husbandmen: and he was abroad for a long time.
Ya gaya wa mutane wannan misali, “Wani mutum ya dasa gonar inabi, ya ba wadansu manoma jinginarta, sai ya tafi wata kasa har ya dade.
10 And at the season he sent a servant to the husbandmen, that they should give him of the fruit of the vineyard. Who, beating him, sent him away empty.
Da lokacin girbi ya yi sai ya aiki wani bawansa zuwa wurin manoman, saboda su bashi daga cikin anfanin gonar. Amma manoman suka doke shi, sai suka kore shi hannu wofi.
11 And again he sent another servant. But they beat him also, and treating him reproachfully, sent him away empty.
Ya aike wani bawa kuma sai suka daddoke shi, suka kunyatar da shi, suka kore shi hannu wofi.
12 And again he sent the third: and they wounded him also, and cast him out.
Ya kuma sake aike na uku suka yi masa rauni, suka jefar da shi a waje.
13 Then the lord of the vineyard said: What shall I do? I will send my beloved son: it may be, when they see him, they will reverence him.
Sai mai gonar inabin ya ce, 'Me zan yi? Zan aiki kaunattacen dana. Watakila zasu ba shi daraja.'
14 Whom when the husbandmen saw, they thought within themselves, saying: This is the heir, let us kill him, that the inheritance may be ours.
Amma sa'adda manoman suka gan shi, suka yi shawara a tsakaninsu, cewa, 'Wannan ne magajin. Bari mu kashe shi, saboda gadon ya zama namu.'
15 So casting him out of the vineyard, they killed him. What therefore will the lord of the vineyard do to them?
Suka jefar da shi waje daga gonar, suka kashe shi. Menene ubangijin gonar inabin zai yi da su?
16 He will come, and will destroy these husbandmen, and will give the vineyard to others. Which they hearing, said to him: God forbid.
Zai zo ya halakar da wadannan manoma, sai ya ba wadansu gonar.” Da suka ji wannan, suka ce, “Allah ya sawake!”
17 But he looking on them, said: What is this then that is written, The stone, which the builders rejected, the same is become the head of the corner?
Amma Yesu ya kalle su, sai yace, “Menene ma'anar wannan nassi? 'Dutsen da magina suka ki, an mayar da shi kan kusurwa'?
18 Whosoever shall fall upon that stone, shall be bruised: and upon whomsoever it shall fall, it will grind him to powder.
Duk wanda ya fadi kan dutsen zai farfashe. Amma duk wanda dutsen ya fadi a kansa, zai rugurguza shi.”
19 And the chief priests and the scribes sought to lay hands on him the same hour: but they feared the people, for they knew that he spoke this parable to them.
Sai marubutan da manyan firistocin suka so su kama shi a wannan sa'a, domin sun sani ya yi wannan misali a kansu ne. Amma sun ji tsoron mutane.
20 And being upon the watch, they sent spies, who should feign themselves just, that they might take hold of him in his words, that they might deliver him up to the authority and power of the governor.
Suna fakonsa, suka aiki magewaya, wadanda suke kamar masu adalci, saboda su sami kuskure cikin maganarsa, don su mika shi ga hukumci da kuma ikon gwamna.
21 And they asked him, saying: Master, we know that thou speakest and teachest rightly: and thou dost not respect any person, but teachest the way of God in truth.
Suka tambaye shi, cewa, “Malam, mun sani da cewa kana fada da koyar da abin ke daidai, kuma ba wanda yake cusa maka ra'ayi, amma kana koyar da gaskiya game da hanyar Allah.
22 Is it lawful for us to give tribute to Caesar, or no?
Wai shin doka ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
23 But he considering their guile, said to them: Why tempt you me?
Amma Yesu ya gane makircinsu, sai ya ce masu,
24 Shew me a penny. Whose image and inscription hath it? They answering, said to him, Caesar’s.
“Nuna mani dinari. Sifar wanene da kuma rubutun wanene akan sa?” Suka ce, “Na Kaisar ne.”
25 And he said to them: Render therefore to Caesar the things that are Caesar’s: and to God the things that are God’s.
Sai ya ce masu, “To sai ku ba Kaisar abin da ke na Kaisar, ku kuma ba Allah, abin da ke na Allah.”
26 And they could not reprehend his word before the people: and wondering at his answer, they held their peace.
Marubutan da manyan firistocin ba su sami abin zargi cikin maganarsa, a gaban mutane ba. Suka yi mamakin amsar sa, ba su kuma ce komai ba.
27 And there came to him some of the Sadducees, who deny that there is any resurrection, and they asked him,
Sa'adda wadansu Sadukiyawa suka zo wurinsa, wadan da suka ce babu tashin mattatu,
28 Saying: Master, Moses wrote unto us, If any man’s brother die, having a wife, and he leave no children, that his brother should take her to wife, and raise up seed unto his brother.
suka tambaye shi, cewa, “Malam, Musa ya rubuta mana cewa idan dan'uwan mutum ya mutu, mai mace kuma ba shi da yaro, sai dan'uwansa ya auri matar, ya samar wa dan'uwansa yaro.
29 There were therefore seven brethren: and the first took a wife, and died without children.
Akwai 'yan'uwa guda bakwai kuma na farin ya yi aure, sai ya mutu babu da,
30 And the next took her to wife, and he also died childless.
haka ma na biyun.
31 And the third took her. And in like manner all the seven, and they left no children, and died.
Na ukun ya aure ta, haka nan na bakwai ma bai bar yaya ba, har suka mutu.
32 Last of all the woman died also.
Daga baya sai matar ma ta mutu.
33 In the resurrection therefore, whose wife of them shall she be? For all the seven had her to wife.
To a ranar tashin mattatu, matar wa za ta zama? Domin duka bakwai din sun aure ta.”
34 And Jesus said to them: The children of this world marry, and are given in marriage: (aiōn g165)
Yesu ya ce masu, “'Ya'yan duniyan nan suna aure, ana kuma ba da su ga aure. (aiōn g165)
35 But they that shall be accounted worthy of that world, and of the resurrection from the dead, shall neither be married, nor take wives. (aiōn g165)
Amma wadanda aka ga cancantarsu a waccan tsara, sun isa su sami tashin mattatu, ba za suyi aure ko a aurar da su ba. (aiōn g165)
36 Neither can they die any more: for they are equal to the angels, and are the children of God, being the children of the resurrection.
Gama ba za su mutu kuma ba, domin suna daidai da mala'iku kuma su 'ya'yan Allah ne, da shike su 'ya'yan tashin matattu ne.
37 Now that the dead rise again, Moses also shewed, at the bush, when he called the Lord, The God of Abraham, and the God of Isaac, and the God of Jacob;
Amma batun tashi matattu, ko Musa ma ya nuna wannan, a cikin jeji, inda ya kira Ubangiji, Allah na Ibrahim da kuma Allah na Ishaku da Allah na Yakubu.
38 For he is not the God of the dead, but of the living: for all live to him.
Yanzu shi ba Allahn matattu ba ne, amma na masu rai, saboda duka suna raye a wurinsa.”
39 And some of the scribes answering, said to him: Master, thou hast said well.
Wadansu marubuta suka amsa, “Malam, ka amsa da kyau.”
40 And after that they durst not ask him any more questions.
Gama ba su sake yi masa wadansu tambayoyi ba.
41 But he said to them: How say they that Christ is the son of David?
Yesu ya ce masu, “Yaya suke cewa Almasihu dan Dauda ne?
42 And David himself saith in the book of Psalms: The Lord said to my Lord, sit thou on my right hand,
Gama Dauda da kansa ya ce a cikin littafin Zabura, Ubangiji ya ce wa Ubangiji na, 'Zauna a hannun dama na,
43 Till I make thy enemies thy footstool.
sai na maida makiyanka a karkashin tafin sawunka.'
44 David then calleth him Lord: and how is he his son?
Dauda ya kira Kristi 'Ubangiji', to ta yaya ya zama dan Dauda?”
45 And in the hearing of all the people, he said to his disciples:
Dukan mutane suna ji ya ce wa almajiransa,
46 Beware of the scribes, who desire to walk in long robes, and love salutations in the marketplace, and the first chairs in the synagogues, and the chief rooms at feasts:
“Ku yi hankali da marubuta, wadanda suna son tafiya da manyan riguna, suna kuma son a gaishe su a cikin kasuwanni, da mayan wuraren zama a cikin majami'u, da kuma manyan wurare a wurin bukukkuwa.
47 Who devour the houses of widows, feigning long prayer. These shall receive greater damnation.
Suna kuma kwace wa gwamraye gidaje, suna kuma badda kama ta wurin yin doguwar addu'a. Wadannan za su sha hukumci mai girma.”

< Luke 20 >