< Lamentations 4 >
1 Aleph. How is the gold become dim, the finest colour is changed, the stones of the sanctuary are scattered in the top of every street?
Zinariya ta rasa kyanta, hasken zinariya ya dushe! An warwatsar da tsarkakakkun duwatsu masu daraja a kan tituna.
2 Beth. The noble sons of Sion, and they that were clothed with the best gold: how are they esteemed as earthen vessels, the work of the potter’s hands?
Dubi samarin Sihiyona masu daraja, waɗanda a dā darajarsu ta isa nauyin zinariya, yanzu ana ɗaukar su a matsayin tukwanen ƙasa, aikin maginin tukwane!
3 Ghimel. Even the sea monsters have drawn out the breast, they have given suck to their young: the daughter of my people is cruel, like the ostrich in the desert.
Ko diloli suna ba’ya’yansu nono su sha, amma mutanena sun zama marasa zuciya kamar jiminai a cikin jeji.
4 Daleth. The tongue of the sucking child hath stuck to the roof of his mouth for thirst: the little ones have asked for bread, and there was none to break it unto them.
Domin ƙishirwa harshen jarirai ya manne a rufin bakinsu; yaran suna roƙo a ba su burodi, amma ba wanda ya ba su.
5 He. They that were fed delicately have died in the streets; they that were brought up in scarlet have embraced the dung.
Waɗanda a dā sukan ci abinci mai daɗi yanzu su ne masu bara a tituna. Waɗanda a dā suke sa kaya masu kyau yanzu suna kwance a kan tarin toka.
6 Vau. And the iniquity of the daughter of my people is made greater than the sin of Sodom, which was overthrown in a moment, and hands took nothing in her.
Horon mutanena ya fi na Sodom girma, wadda aka hallaka farat ɗaya ba wani hannu da ya juya ya taimake ta.
7 Zain. Her Nazarites were whiter than snow, purer than milk, more ruddy than the old ivory, fairer than the sapphire.
’Ya’yan sarakunansu sun fi ƙanƙara haske sun kuma fi madara fari, jikunansu sun fi murjani ja, kyansu kamar shuɗin yakutu.
8 Heth. Their face is now made blacker than coals, and they are not known in the streets: their skin hath stuck to their bones, it is withered, and is become like wood.
Amma yanzu sun fi dare duhu; ba a iya gane su a tituna. Fatar jikinsu ta manne da ƙasusuwansu; sun bushe kamar itace.
9 Teth. It was better with them that were slain by the sword, than with them that died with hunger: for these pined away being consumed for want of the fruits of the earth.
Gara waɗanda aka kashe su da takobi da waɗanda suke mutuwa da yunwa; sun rame domin rashin abinci a gona.
10 Jod. The hands of the pitiful women have sodden their own children: they were their meat in the destruction of the daughter of my people.
Da hannuwansu mata masu tausayi sun dafa yaransu, suka zama masu abinci sa’ad da aka hallaka mutanena.
11 Caph. The Lord hath accomplished his wrath, he hath poured out his fierce anger: and he hath kindled a fire in Sion, and it hath devoured the foundations thereof.
Ubangiji ya saki fushinsa; ya zuba zafin fushinsa. Ya hura wuta a Sihiyona ta kuma cinye harsashin gininta.
12 Lamed. The kings of the earth, and all the inhabitants of the world would not have believed, that the adversary and the enemy should enter in by the gates of Jerusalem.
Sarakunan duniya ba su gaskata ba, haka ma mutanen duniya, cewa magabta da maƙiya za su iya shiga ƙofofin Urushalima.
13 Mem. For the sins of her prophets, and the iniquities of her priests, that have shed the blood of the just in the midst of her.
Amma ya faru domin zunuban annabawanta da muguntar firistocinta, waɗanda suka zub da jinin masu adalci a cikinsu.
14 Nun. They have wandered as blind men in the streets, they were defiled with blood: and when they could not help walking in it, they held up their skirts.
Yanzu suna yawo barkatai a tituna kamar makafi. Sun ƙazantu da jini yadda ba wanda zai kuskura ya taɓa rigunansu.
15 Samech. Depart you that are defiled, they cried out to them: Depart, get ye hence, touch not: for they quarrelled, and being removed, they said among the Gentiles: He will no more dwell among them.
“Ku tafi! Ba ku da tsabta!” Haka mutane suke ihu suke ce musu. “Ku tashi daga nan! Ku tashi daga nan! Kada ku taɓa mu!” Sa’ad da suka gudu suna yawo, mutanen waɗansu ƙasashe suka ce, “Ba za su ci gaba da zama a nan ba.”
16 Phe. The face of the Lord hath divided them, he will no more regard them: they respected not the persons of the priests, neither had they pity on the ancient.
Ubangiji kansa ya warwatsa su; ya daina duban su. Ba a ba firistoci girma, ba su ba dattawa gata.
17 Ain. While we were yet standing, our eyes failed, expecting help for us in vain, when we looked attentively towards a nation that was not able to save.
Idanunmu sun gaji, suna ta dubawa ko taimako zai zo; mu sa ido ko za mu ga ƙasar da za tă iya taimakon mu.
18 Sade. Our steps have slipped in the way of our streets, our end draweth near: our days are fulfilled, for our end is come.
Ana bin sawunmu, ba za mu iya tafiya kan tituna ba. Ƙarshenmu ya kusa, kwanakinmu sun ƙare, gama ƙarshenmu ya zo.
19 Coph. Our persecutors were swifter than the eagles of the air: they pursued us upon the mountains, they lay in wait for us in the wilderness.
Masu fafarar mu sun fi gaggafa mai firiya a sararin sama sauri; sun fafare mu a kan duwatsu suna fakon mu a jeji.
20 Res. The breath of our mouth, Christ the Lord, is taken in our sins: to whom we said: Under thy shadow we shall live among the Gentiles.
Shafaffe na Ubangiji, numfashin ranmu, ya fāɗi cikin tarkonsu. Muna tunani cewa za mu iya rayuwa cikin sauran mutane a ƙarƙashin inuwarsa.
21 Sin. Rejoice, and be glad, O daughter of Edom, that dwellest in the land of Hus: to thee also shall the cup come, thou shalt be made drunk, and naked.
Ku yi murna da farin ciki, ya Diyar Edom, ke mai zama a ƙasar Uz. Amma ke ma za a ba ki kwaf; za ki bugu ki zama tsirara.
22 Thau. Thy iniquity is accomplished, O daughter of Sion, he will no more carry thee away into captivity: he visited thy iniquity, O daughter of Edom, he hath discovered thy sins. The Prayer of Jeremias the Prophet.
Ya Diyar Sihiyona, hukuncinki zai ƙare; ba zai sa zaman bautarki yă yi tsayi ba. Amma ya Diyar Edom, zai hukunta zunubinki yă tona tsiraicinki.