< Judges 15 >
1 And a while after, when the days of the wheat harvest were at hand, Samson came, meaning to visit his wife, and he brought her a kid of the flock. And when he would have gone into her chamber as usual, her father would not suffer him, saying:
Daga baya, a lokacin girbin alkama, Samson ya ɗauki ɗan akuya ya tafi yă ziyarci matarsa. Sai ya ce, “Zan in shiga ɗakin matata.” Amma mahaifinta ya hana shi shiga.
2 I thought thou hadst hated her, and therefore I gave her to thy friend: but she hath a sister, who is younger and fairer than she, take her to wife instead of her.
Ya ce wa, “Na tabbata ba ka sonta sam-sam, don haka na ba da ita ga abokinka. Ba ƙanuwarta ta fi kyau ba? Ka ɗauke ta a maimako.”
3 And Samson answered him: From this day I shall be blameless in what I do against the Philistines: for I will do you evils.
Samson kuwa ya ce musu, “A wannan lokaci ina da iko in rama a kan Filistiyawa; tabbatacce zan ji musu.”
4 And he went and caught three hundred foxes, and coupled them tail to tail, and fastened torches between the tails.
Saboda haka ya tafi ya kama yanyawa ɗari uku ya ɗaura wutsiyoyinsu wutsiya da wutsiya. Sa’an nan ya daure acibalbal a tsakanin ko waɗanne wutsiya biyu,
5 And setting them on fire he let the foxes go, that they might run about hither and thither. And they presently went into the standing corn of the Philistines. Which being set on fire, both the corn that was already carried together, and that which was yet standing, was all burnt, insomuch, that the flame consumed also the vineyards and the oliveyards.
sai ya sa wa acibalbal wuta, ya saki yanyawan suka shiga gonakin Filistiyawa. Suka ƙone dammunan hatsi da hatsin da yake tsaye, tare da gonakin inabi da na zaitun.
6 Then the Philistines said: Who hath done this thing? And it was answered: Samson the son in law of the Thamnathite, because he took away his wife, and gave her to another, hath done these things. And the Philistines went up and burnt both the woman and her father.
Filistiyawa suka yi tambaya suka ce, “Wane ne ya yi wannan abu?” Sai aka ce musu, “Ai, Samson ne surukin mutumin Timna, domin an ba wa abokinsa matarsa.” Saboda haka Filistiyawa suka haura suka je suka ƙone ta da mahaifinta ƙurmus da wuta.
7 But Samson said to them: Although you have done this, yet will I be revenged of you, and then I will be quiet.
Samson ya ce musu, “Tun da kun aikata wannan, ba zan bari ba har sai na ɗau fansa a kanku.”
8 And he made a great slaughter of them, so that in astonishment they laid the calf of the leg upon the thigh. And going down he dwelt in a cavern of the rock Etam.
Ya kuwa fāɗa musu ya kuma karkashe su da yawa. Sa’an nan ya gangara ya zauna a kogo a dutsen Etam.
9 Then the Philistines going up into the land of Juda, camped in the place which afterwards was called Lechi, that is, the Jawbone, where their army was spread.
Filistiyawa suka haura suka yi sansani a Yahuda, suka bazu kusa da Lehi.
10 And the men of the tribe of Juda said to them: Why are you come up against us? They answered: We are come to bind Samson, and to pay him for what he hath done against us.
Mutanen Yahuda suka ce, “Me ya sa kuka zo mana da yaƙi?” Sai suka ce, “Mun zo ne mu kama Samson, a matsayin fursunan yaƙi, mu yi masa kamar yadda ya yi mana.”
11 Wherefore three thousand men of Juda, went down to the cave of the rock Etam, and said to Samson: Knowest thou not that the Philistines rule over us? Why wouldst thou do thus? And he said to them: As they did to me, so have I done to them.
Sa’an nan mutane dubu uku daga Yahuda suka gangara wajen Samson a kogo a dutsen Etam. Suka ce masa, “Ba ka san cewa Filistiyawa ne suke mulkinmu ba? Me ke nan ka yi mana?” Ya ce musu, “Na ɗan yi musu abin da suka yi mini ne.”
12 And they said to him, We are come to bind thee and to deliver thee into the hands of the Philistines. And Samson said to them: Swear to me, and promise me, that you will not kill me.
Suka ce masa, “To, mun zo ne mu daure ka mu kai wa Filistiyawa.” Samson ya ce, “Ku rantse mini ba za ku kashe ni da kanku ba.”
13 They said: We will not kill thee: but we will deliver thee up bound. And they bound him with two new cords, and brought him from the rock Etam.
Suka ce, “Mun yarda, za mu dai daure ka mu ba da kai gare su. Ba za mu kashe ka ba.” Saboda haka suka daure shi da sababbin igiyoyi biyu, suka saukar da shi daga dutsen.
14 Now when he was come to the place of the Jawbone, and the Philistines shouting went to meet him, the spirit of the Lord came strongly upon him: and as the flax is wont to be consumed at the approach of fire, so the bands with which he was bound were broken and loosed.
Yayinda ya zo gab da Lehi, sai Filistiyawa suka sheƙo a guje da ihu suka nufo shi. Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko da iko a kansa. Igiyoyin da suke daure a hannuwansa kuwa suka zama kamar abin da wuta ta babbaka, suka tsintsinke suka zuba daga hannuwansa.
15 And finding a jawbone, even the jawbone of an ass which lay there, catching it up, be slew therewith a thousand men.
Da ya samo muƙamuƙin jaki, ya ɗauka, sai ya karkashe mutane dubu ɗaya.
16 And he said: With the jawbone of an ass, with the jaw of the colt of asses I have destroyed them, and have slain a thousand men.
Sa’an nan Samson ya ce, “Da muƙamuƙin jaki na mai da su jakuna. Da muƙamuƙin jaki na kashe mutum dubu.”
17 And when he had ended these words singing, he threw the jawbone out of his hand, and called the name of that place Ramathlechi, which is interpreted the lifting up of the jawbone.
Da ya gama magana, sai ya jefar da muƙamuƙin; aka ba wa wannan wuri suna Ramat Lehi.
18 Arid being very thirsty, he cried to the Lord, and said: Thou hast given this very great deliverance and victory into the hand of thy servant: and behold I die for thirst, and shall fall into the hands of the uncircumcised.
Saboda ƙishirwa ta kama shi ƙwarai, sai ya ce wa Ubangiji, “Ka ba bawanka wannan babbar nasara. To, sai in mutu da ƙishirwa, har in shiga a hannun marasa kaciyan nan su kashe ni?”
19 Then the Lord opened a great tooth in the jaw of the ass, and waters issued out of it. And when he had drank them he refreshed his spirit, and recovered his strength. Therefore the name of that place was called, The Spring of him that invoked from the jawbone, until this present day.
Sa’an nan Allah ya buɗe wani rami a Lehi, ruwa kuwa ya fito daga ciki. Da Samson ya sha, sai ƙarfinsa ya dawo, ya kuma wartsake. Aka sa wa wannan maɓulɓula suna En Hakkore, yana nan a Lehi har wa yau.
20 And he judged Israel in the days of the Philistines twenty years.
Samson kuwa ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin a zamanin Filistiyawa.