< Joshua 7 >
1 But the children of Israel transgressed the commandment, and took to their own use of the anathema. For Achan the son of Charmi, the son of Zabdi, the son of Zare of the tribe of Juda, took something of the anathema: and the Lord was angry against the children of Israel.
Amma Isra’ilawa ba su yi aminci game da kayan da aka hallaka ba; Akan ɗan Karmi, ɗan Zabdi, ɗan Zera, na kabilan Yahuda ya kwashi waɗansu abubuwa, saboda haka fushin Ubangiji ya sauka a kan Isra’ilawa.
2 And when Josue sent men from Jericho against Hai, which is beside Bethaven, on the east side of the town of Bethel, he said to them: Go up, and view the country: and they fulfilled his command, and viewed Hai.
Sai Yoshuwa ya aika mutane daga Yeriko zuwa Ai kusa da Bet-Awen gabas da Betel, ya ce musu, “Ku je ku leƙo ku ga yadda yankin yake.” Sai mutanen suka je suka leƙo asirin ƙasar Ai.
3 And returning they said to him: Let not all the people go up, but let two or three thousand men go and destroy the city: why should all the people be troubled in vain against enemies that are very few?
Da suka dawo wurin Yoshuwa suka ce, “Ba lalle dukan jama’a su je yaƙi da Ai ba, ka aika mutum dubu biyu ko dubu uku su je su ciwo ƙasar da yaƙi, ba sai ka dami mutane duka ba, gama mutanen wurin kaɗan ne.”
4 There went up therefore three thousand fighting men: who immediately turned their backs,
Saboda haka sai kimanin mutum duba uku suka haura; amma mutanen Ai suka fatattake su,
5 And were defeated by the men of the city of Hai, and there fell of them six and thirty men: and the enemies pursued them from the gate as far as Sabarim, and they slew them as they fled by the descent: and the heart of the people was struck with fear, and melted like water.
suka kashe Isra’ilawa wajen mutum talatin da shida, suka fafari Isra’ilawa tun daga bakin ƙofar birnin har zuwa wurin da ake fasa duwatsu. Suka karkashe su a gangare. Wannan ya sa zuciyar Isra’ilawa ta narke suka zama kamar ruwa.
6 But Josue rent his garments, and fell flat on the ground before the ark of the Lord until the evening, both he and all the ancients of Israel: and they put dust upon their heads.
Sai Yoshuwa ya yaga tufafinsa ya fāɗi rubda ciki a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, yana can har yamma. Dattawan Isra’ila ma suka yi haka, suka zuba toka a kawunansu.
7 And Josue said: Alas, O Lord God, why wouldst thou bring this people over the river Jordan, to deliver us into the hand of the Amorrhite, and to destroy us? would God, we had stayed beyond the Jordan as we began.
Yoshuwa kuma ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, me ya sa ka sa mutanen nan suka ƙetare Urdun don ka bari mu shiga hannun Amoriyawa su hallaka mu? Kila da mun haƙura mun zauna a ɗaya gefen Urdun da ya fi mana!
8 My Lord God, what shall I say, seeing Israel turning their backs to their enemies?
Ya Ubangiji me zan ce, yanzu da abokan gāban Isra’ilawa suka ci ƙarfinsu?
9 The Chanaanites, and all the inhabitants of the land will hear of it, and being gathered together will surround us and cut off our name from the earth: and what wilt thou do to thy great name?
Yanzu Kan’aniyawa da sauran jama’a za su ji, za su zo su kewaye mu su share sunanmu daga duniya. To, yanzu me za ka yi don girman sunanka?”
10 And the Lord said to Josue: Arise, why liest thou flat on the ground?
Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka tashi! Me kake yi kwance rubda ciki?
11 Israel hath sinned, and transgressed my covenant: and they have taken of the anathema, and have stolen and lied, and have hidden it among their goods.
Isra’ilawa sun yi zunubi, sun karya sharaɗin da na yi musu. Sun ɗauki waɗansu abubuwan da aka keɓe; sun yi sata, sun yi ƙarya, sun ɓoye su cikin kayansu.
12 Neither can Israel stand before his enemies, but he shall flee from them: because he is defiled with the anathema. I will be no more with you, till you destroy him that is guilty of this wickedness.
Shi ne ya sa Isra’ilawa suka kāsa yin tsayayya da abokan gābansu; suka juya suka gudu domin za a hallaka su. Ba zan sāke kasancewa tare da ku ba sai in kun hallaka duk abin da aka keɓe don hallaka.
13 Arise, sanctify the people, and say to them: Be ye sanctified against tomorrow: for thus saith the Lord God of Israel: The anathema is in the midst of thee, O Israel: thou canst not stand before thy enemies, till he be destroyed out of thee that is defiled with this wickedness.
“Tashi, ka je ka tsarkake mutane. Ka ce musu su tsarkake kansu, su yi shiri domin gobe; gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, a cikinku akwai abubuwan da aka keɓe, ya Isra’ilawa. Ba za ku iya yin tsayayya da abokan gābanku ba sai in kun rabu da abubuwan nan da aka haramta.
14 And you shall come in the morning every one by your tribes: and what tribe soever the lot shall find, it shall come by its kindreds and the kindred by its houses, and the house by the men.
“‘Da safe ku zo kabila-kabila. Kabilar da Ubangiji ya ware, za tă zo gaba gida-gida; gidan da Ubangiji ya ware, za su zo gaba iyali-iyali. Iyalin kuma da Ubangiji ya ware, za su zo gaba mutum bayan mutum.
15 And whosoever he be that shall be found guilty of this fact, he shall be burnt with fire with all his substance, because he hath transgressed the covenant of the Lord, and hath done wickedness in Israel.
Mutumin da aka same shi da haramtattun abubuwan kuwa za a ƙone shi, duk da mallakarsa domin ya karya sharaɗin da Ubangiji ya yi muku, ya yi abin kunya a Isra’ila!’”
16 Josue, therefore, when he rose in the morning, made Israel to come by their tribes, and the tribe of Juda was found,
Kashegari da sassafe Yoshuwa ya sa Isra’ilawa suka fito kabila-kabila, aka ware kabilar Yahuda.
17 Which being brought by its families, it was found to be the family of Zare. Bringing that also by the houses, he found it to be Zabdi.
Gidan Yahuda suka zo gaba, sai aka ware gidan Zera, aka sa suka fito iyali-iyali, sai aka ware Zabdi.
18 And bringing his house man by man, he found Achan the son of Charmi, the son of Zabdi, the son of Zare of the tribe of Juda.
Yoshuwa kuwa ya sa iyalin Zabdi suka fito mutum-mutum, sai kuwa aka ware Akan ɗan Karmi, ɗan Zimri, ɗan Zera na kabilar Yahuda.
19 And Josue said to Achan: My son, give glory to the Lord God of Israel, and confess, and tell me what thou hast done, hide it not.
Sai Yoshuwa ya ce wa Akan, “Ɗana, sai ka ba Ubangiji, Allah na Isra’ila ɗaukaka, ka yi masa yabo. Ka gaya mini abin da ka yi; kada ka ɓoye mini.”
20 And Achan answered Josue, and said to him: Indeed I have sinned against the Lord the God of Israel, and thus and thus have I done.
Akan kuwa ya amsa ya ce, “Gaskiya ne! Na yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila zunubi. Ga abin da na yi.
21 For I saw among the spoils a scarlet garment exceeding good, and two hundred sides of silver, and a golden rule of fifty sides: and I coveted them, and I took them away, and hid them in the ground is the midst of my tent, and the silver I covered with the earth that I dug up.
A cikin ganimar, na ga doguwar riga mai kyau irin ta Babilon, da shekel ɗari biyu na azurfa, da kuma sandan zinariya mai nauyin shekel hamsin, sai raina ya so su, na kuwa kwashe su. Na tona rami a cikin ƙasa a tentina; na ɓoye.”
22 Josue therefore sent ministers: who running to his tent, found all hidden in the same place, together with the silver.
Sai Yoshuwa ya aiki’yan aika suka tafi da gudu zuwa tenti ɗin, haka kuwa suka same su a ɓoye a tentinsa, da azurfa a ƙarƙashi.
23 And taking them away out of the tent, they brought them to Josue, and to all the children of Israel, and threw them down before the Lord.
Suka kwashe kayan daga tenti ɗin suka kawo wa Yoshuwa da sauran Isra’ilawa, suka baza su a gaban Ubangiji.
24 Then Josue and all Israel with him took Achan the son of Zare, and the silver and the garments, and the golden rule, his sons also and his daughters, his oxen and asses and sheep, the tent also, and all the goods: and brought them to the valley of Achor:
Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ɗauki Akan ɗan Zera, da azurfar, doguwar rigar, sandan zinariya,’ya’yansa maza da mata, shanunsa, jakuna da tumaki, tentinsa da duk abin da yake da shi, suka kai su Kwarin Akor.
25 Where Josue said: Because thou hast troubled us, the Lord trouble thee this day. And all Israel stoned him: and all things that were his, were consumed with fire.
Yoshuwa ya ce, “Me ya sa ka jawo mana wahala haka? Ubangiji zai kawo maka wahala kai ma a yau.” Sai dukan Isra’ilawa suka jajjefe shi, bayan da suka gama jifarsa sai suka ƙone sauran.
26 And they gathered together upon him a great heap of stones, which remaineth until this present day. And the wrath of the Lord was turned away from them. And the name of that place was called the Valley of Achor, until this day.
Suka tara manyan duwatsu a kan Akan, tarin duwatsun na nan a can har wa yau. Sa’an nan Ubangiji ya huce daga fushinsa mai zafi. Saboda haka ake kiran wurin Kwarin Akor.