< Joshua 23 >
1 And when a long time was passed, after that the Lord had given peace to Israel, all the nations round about being subdued, and Josue being now old, and far advanced in years:
An daɗe bayan da Ubangiji ya ba Isra’ilawa hutu daga dukan abokan gāban da suke kewaye da su. Yoshuwa kuwa ya tsufa, shekarunsa sun yi yawa,
2 Josue called for all Israel, and for the elders, and for the princes, and for the judges, and for the masters, and said to them: I am old, and far advanced in years:
sai ya aika a kira Isra’ilawa duka, dattawansu, shugabanninsu, alƙalansu, da manyan ma’aikatansu, ya ce musu, “Na tsufa, shekaruna kuwa sun yi yawa,
3 And you see all that the Lord your God hath done to all the nations round about, how he himself hath fought for you:
ku kanku kun ga dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi da idanunku wa dukan ƙasashen nan, Ubangiji Allahnku shi ne wanda ya yi yaƙi dominku.
4 And now since he hath divided to you by lot all the land, from the east of the Jordan unto the great sea, and many nations yet remain:
Ku tuna yadda na rarraba wa kabilanku ƙasashen nan su zama naku na gādo, dukan ƙasashen da suka rage, ƙasashen da na ci da yaƙi, tsakanin Urdun da Bahar Rum a yamma.
5 The Lord your God will destroy them, and take them away from before your face, and you shall possess the land as he hath promised you.
Ubangiji Allahnku kansa zai kore su a madadinku. Zai fafare su a gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu, yadda Ubangiji Allah ya yi muku alkawari.
6 Only take courage, and be careful to observe all things that are written in the book of the law of Moses: and turn not aside from them neither to the right hand nor to the left:
“Ku yi ƙarfin hali, ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan abin da aka rubuta a cikin Littafin Dokoki na Musa, ba tare da kun juya hagu ko dama ba.
7 Lest after that you are come in among the Gentiles, who will remain among you, you should swear by the name of their gods, and serve them, and adore them:
Kada ku haɗa kai da mutanen nan da suke zama cikinku; ba ruwanku da sunayen allolinsu, kada ku rantse da su. Kada kuwa ku bauta musu ko kuwa ku rusuna musu.
8 But cleave ye unto the Lord your God: as you have done until this day.
Sai dai ku riƙe Ubangiji Allahnku da kyau, yadda kuka yi har zuwa yanzu.
9 And then the Lord God will take away before your eyes nations that are great and very strong, and no man shall be able to resist you.
“Ubangiji ya kori manyan ƙasashe masu ƙarfi; har wa yau ba wanda ya iya cin ku da yaƙi.
10 One of you shall chase a thousand men of the enemies: because the Lord your God himself will fight for you, as he hath promised.
Mutum ɗaya a cikinku ya isa yă sa mutane dubu nasu su gudu, domin Ubangiji Allahnku yana yaƙi dominku, kamar yadda ya yi alkawari.
11 This only take care of with all diligence, that you love the Lord your God.
Saboda haka sai ku kula da kanku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku.
12 But if you will embrace the errors of these nations that dwell among you, and make marriages with them, and join friendships:
“Amma in kuka juya baya kuka zama abokai ga waɗanda suka ragu suke zama a cikinku a ƙasashen nan, har kuka yi auratayya da su, kuka haɗa kai da su,
13 Know ye for a certainty that the Lord your God will not destroy them before your face, but they shall be a pit and a snare in your way, and a stumblingblock at your side, and stakes in your eyes, till he take you away and destroy you from off this excellent land, which he hath given you.
ku tabbata cewa Ubangiji Allahnku ba zai kore muku mutanen ƙasashen nan ba, sai ma su zama muku dutsen tuntuɓe da tarko, za su zama bulala a bayanku, ƙayayyuwa a idanunku, har sai kun hallaka daga wannan ƙasa mai kyau wadda Ubangiji Allahnku ya ba ku.
14 Behold this day I am going into the way of all the earth, and you shall know with all your mind that of all the words which the Lord promised to perform for you, not one hath failed.
“Yanzu na kusa barin fuskar duniyan nan. Kun sani da dukan zuciyarku, da dukan ranku cewa, Ba ko ɗaya daga cikin alkawuran da Ubangiji Allahnku ya yi, da bai cika ba. Kowane alkawari ya cika; ba ko ɗaya da bai cika ba.
15 Therefore as he hath fulfilled in deed, what he promised, and all things prosperous have come: so Will he bring upon you all the evils he hath threatened, till he take you away and destroy you from off this excellent land, which he hath given you,
Kamar yadda Ubangiji Allahnku kuwa ya cika kowane alkawari mai kyau, haka ma ba zai fasa kawo muku bala’in da ya faɗi ba, sai ya hallaka ku daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba ku.
16 When you shall have transgressed the covenant of the Lord your God, which he hath made with you, and shall have served strange gods, and adored them: then shall the indignation of the Lord rise up quickly and speedily against you, and you shall be taken away from this excellent land, which he hath delivered to you.
In kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku wanda ya umarce ku, in kuka je kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka rusuna musu, fushin Ubangiji zai sauko a kanku, za ku kuwa hallaka da sauri daga ƙasan nan mai kyau da ya ba ku.”