< Joshua 13 >

1 Josue was old, and far advanced in years, and the Lord said to him: Thou art grown old, and advanced in age, and there is a very large country left, which is not yet divided by lot:
Sa’ad da Yoshuwa ya tsufa, Ubangiji ya ce masa, “Ka tsufa ƙwarai, ga shi kuma akwai sauran ƙasa mai fāɗi da ba ku riga kun mallaka ba.
2 To wit, all Galilee, Philistia, and all Gessuri.
“Ga ƙasar da ta rage, “dukan yankunan Filistiyawa da na Geshurawa.
3 From the troubled river, that watereth Egypt, unto the borders of Accaron northward: the land of Chanaan, which is divided among the lords of the Philistines, the Gazites, the Azotians, the Ascalonites, the Gethites, and the Accronites.
Daga Kogin Shihor a gabashin Masar zuwa sashen Ekron a arewa, dukan wannan ƙasa ana lissafta ta a cikin ƙasar Kan’aniyawa, ko da yake tana a sashen da sarakuna biyar na Filistiyawa na Gaza, Ashdod, Ashkeloniyawa, Gat da Ekron; na Awwiyawa.
4 And on the south side are the Hevites, all the land of Chanaan, and Maara of the Sidonians as far as Apheca, and the borders of the Amorrhite,
Daga wajen kudu kuma, dukan ƙasar Kan’aniyawa ce. Iyakarta a arewa ta fara daga Ara ta Sidoniyawa har zuwa Afek, ta zarce har zuwa iyakar Amoriyawa;
5 And his confines. The country also of Libanus towards the east from Baalgad under mount Hermon to the entering into Emath.
da ƙasar Gebaliyawa; da dukan Lebanon wajen gabas daga Ba’al-Gad a gindin Dutsen Hermon zuwa Lebo Hamat.
6 Of all that dwell in the mountains from Libanus, to the waters of Maserephoth, and all the Sidonians. I am he that will cut them off from before the face of the children of Israel. So let their land come in as a part of the inheritance of Israel, as I have commanded thee.
“Dukan mazauna kan yankunan tuddai daga Lebanon zuwa Misrefot Mayim, wato, dukan Sidoniyawa, ni da kaina zan kore su a gaban Isra’ilawa. Ka tabbata ka raba wa Isra’ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka,
7 And now divide the land in possession to the nine tribes, and to the half tribe of Manasses,
ka raba ta tă zama gādo wa kabilu tara da kuma rabin kabilar Manasse.”
8 With whom Ruben and Gad have possessed the land, which Moses the servant of the Lord delivered to them beyond the river Jordan, on the east side.
Rabin kabilar Manasse, mutanen Ruben da mutanen Gad suka karɓi rabonsu na gādo wanda Musa ya ba su a gabashin Urdun. Abin da Musa bawan Ubangiji ya ba su ke nan.
9 From Aroer, which is upon the bank of the torrent Amen, and in the midst of the valley and all the plains of Medaba, as far as Dibon:
Wannan ya tashi daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, ya kuma haɗa da ƙasar da take tudun Medeba har zuwa Dibon,
10 And all the cities of Sehon, king of the Amorrhites, who reigned in Hesebon, unto the borders of the children of Ammon.
da dukan garuruwan Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon, har zuwa iyakar Ammonawa.
11 And Galaad, and the borders of Gessuri and Machati, and all mount Hermon, and all Basan as far as Salecha,
Haɗe da Gileyad, inda mutanen Geshur da Ma’aka suke. Dukan Dutsen Hermon, da dukan Bashan har zuwa Saleka,
12 All the kingdom of Og in Basan, who reigned in Astaroth and Edrai, he was of the remains of the Raphaims: and Moses overthrew and destroyed them.
wato, dukan masarautar Og a Bashan, wanda ya yi mulkin Ashtarot da Edireyi, yana cikin waɗanda suke na ƙarshe da ba a kashe ba a cikin Refahiyawa. Musa ya ci su da yaƙi, ya ƙwace ƙasarsu.
13 And the children of Israel would not destroy Gessuri and Machati: and they have dwelt in the midst of Israel, until this present day.
Amma Isra’ilawa ba su kori mutanen Geshur da Ma’aka ba, saboda haka suka ci gaba da zama cikin Isra’ilawa har wa yau.
14 But to the tribe of Levi he gave no possession: but the sacrifices and victims of the Lord God of Israel, are his inheritance, as he spoke to him.
Kabilar Lawiyawa ne kaɗai Musa bai ba ta gādo ba, gama hadayun ƙonawa da ake miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
15 And Moses gave a possession to the children of Ruben according to their kindreds.
Ga abin da Musa ya ba kabilar Ruben bisa ga iyalansu.
16 And their border was from Aroer, which is on the bank of the torrent Arnon, and in the midst of the valley of the same torrent: all the plain, that leadeth to Medaba,
Abin da ya kama daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba
17 And Hesebon, and all their villages, which are in the plains. Dibon also, and Bamothbaal, and the town of Baalmaon,
zuwa Heshbon, da dukan garuruwan kan tudu, haɗe da Dibon, Bamot Ba’al, Bet-Ba’al-Meyon,
18 And Jassa, and Cidimoth, and Mephaath,
Yahza, Kedemot, Mefa’at,
19 And Cariathaim, and Sabama, and Sarathasar in the mountain of the valley.
Kiriyatayim, Sibma, Zeret Shahar kan tudu cikin kwari,
20 Bethphogor and Asedoth, Phasga and Bethiesimoth,
Bet-Feyor, gangaren Fisga da Bet-Yeshimot,
21 And all the cities of the plain, and all the kingdoms of Sehon king of the Amorrhites, that reigned in Hesebon, whom Moses slew with the princes of Madian: Hevi, and Recem, and Sur and Hur, and Rebe, dukes of Sehon inhabitants of the land.
dukan garuruwan da suke kan tudu da dukan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Musa ya yi nasara da shi, da shugabannin Midiyawa, wato, Ewi, Rekem, Zur, Hur, da Reba, sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar.
22 Balaam also the son of Beer the soothsayer, the children of Israel slew with the sword among the rest that were slain.
Ƙari a kan waɗanda aka kashe a yaƙi, Isra’ilawa suka kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi don yana duba.
23 And the river Jordan was the herder of the children of Ruben. This is the possession of the Rubenites, by their kindreds, of cities and villages.
Gefen Urdun shi ne iyakar mutanen Ruben. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon mutanen Ruben, bisa ga iyalansu.
24 And Moses gave to the tribe of Gad and to his children by their kindreds a possession, of which this is the division.
Ga abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalansu.
25 The border of Jaser, and all the cities of Galaad, and half the land of the children of Ammon: as far as Aroer which is over against Rabba:
Yankin ƙasarsu ya ƙunshi Yazer, da dukan garuruwan Gileyad, da rabin ƙasar Ammonawa har zuwa Arower kusa da Rabba,
26 And from Hesebon unto Ramoth, Masphe and Betonim: and from Manaim unto the borders of Dabir.
da kuma daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, da kuma daga Mahanayim zuwa sashen Debir,
27 And in the valley Betharan and Bethnemra, and Socoth, and Saphon the other part of the kingdom of Sehon king of Hesebon: the limit of this also is the Jordan, as far as the uttermost part of the sea of Cenereth beyond the Jordan on the east side.
kuma a cikin kwari, Bet-Haram, Bet-Nimra, Sukkot da Zafon da kuma sauran masarautar Sihon sarkin Heshbon (gabashin Urdun, abin da ya kama har zuwa ƙarshen Tekun Kinneret).
28 This is the possession of the children of Gad by their families, their cities, and villages.
Waɗannan garuruwan da ƙauyukansu duka, gādon mutanen Gad ne, bisa ga iyalansu.
29 He gave also to the half tribe of Manasses and his children possession according to their kindreds,
Ga abin da Musa ya ba rabin kabilar Manasse, wato, wa rabin zuriyar Manasse, bisa ga iyalansu.
30 The beginning whereof is this: from Manaim all Basan, and all the kingdoms of Og king of Basan, and all the villages of Jair, which are in Basan, threescore towns.
Abin da ya miƙe daga Mahanayim haɗe da dukan Bashan, da gefen masarautar Og sarkin Bashan, da dukan garuruwan Yayir guda sittin da suke a Bashan,
31 And half Galaad, and Astaroth, and Edrai, cities of the kingdom of Og in Basan: to the children of Machir, the son of Manasses, to one? half of the children of Machir according to their kindreds.
da rabin Gileyad, da Ashtarot, Edireyi (biranen sarki Og a Bashan). Wannan shi ne rabon da zuriyar Makir ɗan Manasse suka samu, domin rabin’ya’yan Makir maza, bisa ga iyalansu.
32 This possession Moses divided in the plains of Moab, beyond the Jordan, over against Jericho on the east side.
Waɗannan su ne rabon gādon da Musa ya yi lokacin da suke cikin filayen Mowab a hayin gabashin Urdun kusa da Yeriko.
33 But to the tribe of Levi he gave no possession: because the Lord the God of Israel himself is their possession, as he spoke to them.
Amma Musa bai ba kabilar Lawiyawa gādo ba; Ubangiji, Allah na Isra’ila, shi ne gādonsu kamar yadda ya yi musu alkawari.

< Joshua 13 >