< Joel 2 >
1 Blow ye the trumpet in Sion, sound an alarm in my holy mountain, let all the inhabitants of the land tremble: because the day of the Lord cometh, because it is nigh at hand,
Ku busa ƙaho a cikin Sihiyona; ku yi karar amo a tsaunina mai tsarki. Bari dukan mazaunan ƙasar su yi rawan jiki, gama ranar Ubangiji tana zuwa. Tana gab da faruwa
2 A day of darkness, and of gloominess, a day of clouds and whirlwinds: a numerous and strong people as the morning spread upon the mountains: the like to it hath not been from the beginning, nor shall be after it even to the years of generation and generation.
rana ce ta baƙin duhu ƙirin, ranar gizagizai ce baƙi ƙirin. Babbar rundunar mayaƙa mai ƙarfi tana zuwa kamar ketowar alfijir a kan duwatsu yadda ba a taɓa ganin irinta ba, ba kuwa za a ƙara ganin irinta ba har tsararraki masu zuwa.
3 Before the face thereof a devouring fire, and behind it a burning flame: the land is like a garden of pleasure before it, and behind it a desolate wilderness, neither is there any one that can escape it.
A gabansu wuta tana ci, a bayansu ga harshen wuta yana ci, A gabansu ƙasa ta yi kamar gonar Eden, a bayansu kuma jeji ne wofi, babu abin da ya kuɓuce musu.
4 The appearance of them is as the appearance of horses, and they shall run like horsemen.
Suna da kamannin dawakai; suna gudu kamar dokin yaƙi.
5 They shall leap like the noise of chariots upon the tops of mountains, like the noise of a flame of fire devouring the stubble, as a strong people prepared to battle.
Da motsi kamar na kekunan yaƙi sun tsallake ƙwanƙolin duwatsu, kamar ƙarar harshen wuta mai cin tattaka, kamar runduna mai ƙarfi wadda ta ja dāgār yaƙi.
6 At their presence the people shall be in grievous pains: all faces shall be made like a kettle.
Da ganinsu, al’ummai sun kamu da azaba; kowace fuska ta yanƙwane.
7 They shall run like valiant men: like men of war they shall scale the wall: the men shall march every one on his way, and they shall not turn aside from their ranks.
Sukan auka kamar jarumawa; sukan hau katanga kamar sojoji. Kowa yana takawa bisa ga tsari, ba mai kaucewa.
8 No one shall press upon his brother: they shall walk every one in his path: yea, and they shall fall through the windows, and shall take no harm.
Ba sa turin juna, kowane yakan miƙe gaba. Sukan kutsa cikin abokan gāba ba mai tsai da su.
9 They shall enter into the city: they shall run upon the wall, they shall climb up the houses, they shall come in at the windows as a thief.
Sukan ruga cikin birni, suna gudu a kan katanga. Sukan hau gidaje, sukan shiga ta tagogi kamar ɓarayi.
10 At their presence the earth hath trembled, the heavens are moved: the sun and moon are darkened, and the stars have withdrawn their shining.
A gabansu duniya takan girgiza, sararin sama kuma yakan jijjigu, rana da wata su yi duhu, taurari kuma ba sa ba da haske.
11 And the Lord hath uttered his voice before the face of his army: for his armies are exceeding great, for they are strong and execute his word: for the day of the Lord is great and very terrible: and who can stand it?
Ubangiji ya yi tsawa wa shugaban mayaƙansa; sojojinsa sun fi a ƙirge masu ƙarfi ne kuma su waɗanda suke biyayya da umarninsa. Ranar Ubangiji da girma take; mai banrazana. Wa zai iya jure mata?
12 Now therefore saith the Lord: Be converted to me with all your heart, in fasting, and in weeping, and in mourning.
“Ko yanzu”, in ji Ubangiji, “Ku juyo gare ni da dukan zuciyarku, da azumi da kuka da makoki.”
13 And rend your hearts, and not your garments, and turn to the Lord your God: for he is gracious and merciful, patient and rich in mercy, and ready to repent of the evil.
Ku kyakkece zuciyarku ba rigunanku ba. Ku juyo ga Ubangiji Allahnku, gama shi mai alheri ne mai tausayi kuma mai jinkirin fushi da yawan ƙauna, yakan kuma janye daga aika da bala’i.
14 Who knoweth but he will return, and forgive, and leave a blessing behind him, sacrifice and libation to the Lord your God?
Wa ya sani? Ko zai juya yă kuma ji tausayi yă sa mana albarka ta wurin hadaya ta gari da hadaya ta sha wa Ubangiji Allahnku.
15 Blow the trumpet in Sion, sanctify a fast, call a solemn assembly,
A busa ƙaho a Sihiyona, a yi shelar azumi mai tsarki, a kira tsarkakan taro.
16 Gather together the people, sanctify the church, assemble the ancients, gather together the little ones, and them that suck at the breasts: let the bridegroom go forth from his bed, and the bride out of her bride chamber.
A tattara mutane; ku tsarkake taron; ku kawo dattawa wuri ɗaya; ku kuma tara yara, da waɗanda suke shan mama. Bari ango yă bar ɗakinsa amarya kuma lolokinta.
17 Between the porch and the altar the priests the Lord’s ministers shall weep, and shall say: Spare, O Lord, spare thy people: and give not thy inheritance to reproach, that the heathen should rule over them. Why should they say among the nations: Where is their God?
Bari firistocin da suke yin hidima a gaban Ubangiji, su yi kuka tsakanin filin haikali da bagade. Bari su ce, “Ka cece mutanenka, ya Ubangiji. Kada ka bar gādonka yă zama abin dariya, da abin ba’a a cikin al’ummai. Me zai sa a ce a cikin mutane, ‘Ina Allahnsu yake?’”
18 The Lord hath been zealous for his land, and hath spared his people.
Ta haka Ubangiji zai yi kishin ƙasarsa yă kuma ji tausayin mutanensa.
19 And the Lord answered and said to his people: Behold I will send you corn, and wine, and oil, and you shall be filled with them: and I will no more make you a reproach among the nations.
Ubangiji zai amsa musu ya ce, “Ina aika da hatsi, sabon ruwan inabi, da mai, isashe da zai ƙosar da ku sosai; ba kuma zan ƙara maishe ku abin dariya ga al’ummai ba.
20 And I will remove far off from you the northern enemy: and I will drive him into a land unpassable, and desert, with his face towards the east sea, and his hinder part towards the utmost sea: and his stench shall ascend, and his rottenness shall go up, because he hath done proudly.
“Zan kori sojojin arewa nesa da ku, in tura su cikin busasshiyar ƙasa marar amfani kuma, kuma da sawunsu na gaba zan tura su zuwa gabashin teku da kuma sawunsu na baya tura su zuwa yammanci a Bahar Rum. Warinsu kuma zai bazu; ɗoyinsu zai tashi.” Tabbatacce ya yi al’amura masu girma.
21 Fear not, O land, be glad and rejoice: for the Lord hath done great things.
Kada ki ji tsoro, ya ƙasa; ki yi murna ki kuma yi farin ciki. Tabbatacce Ubangiji ya yi abubuwa masu girma.
22 Fear not, ye beasts of the fields: for the beautiful places of the wilderness are sprung, for the tree hath brought forth its fruit, the fig tree, and the vine have yielded their strength.
Kada ku ji tsoro, ya ku namun jeji, gama wuraren kiwo sun yi kore shar. Itatuwa suna ba da’ya’yansu; itacen ɓaure da na inabi suna ba da amfaninsu.
23 And you, O children of Sion, rejoice, and be joyful in the Lord your God: because he hath given you a teacher of justice, and he will make the early and the latter rain to come down to you as in the beginning.
Ku yi murna, ya ku mutanen Sihiyona, ku yi farin ciki cikin Ubangiji Allahnku, gama ya ba ku ruwan bazara cikin adalci. Yakan aika muku yayyafi a yalwace, na bazara da na kaka, kamar dā.
24 And the floors shall be filled with wheat, and the presses shall overflow with wine and oil.
Masussukai za su cika da hatsi; randuna za su cika da sabon ruwan inabi da mai suna zuba.
25 And I will restore to you the ears which the locust, and the bruchus, and the mildew, and the palmerworm have eaten; my great host which I sent upon you.
“Zan mayar muku da abin da fāra suka ci a waɗannan shekaru waɗanda ɗango da fāra masu gaigayewa, da kuma sauran fāra da tarin fāra babban mayaƙan da na aika don su fāɗa muku.
26 And you shall eat in plenty, and shall be filled: and you shall praise the name of the Lord your God, who hath done wonders with you, and my people shall not be confounded for ever.
Za ku sami a wadace ku ci, har sai kun ƙoshi, za ku kuma yabi sunan Ubangiji Allahnku, wanda ya yi muku ayyukan banmamaki; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
27 And you shall know that I am in the midst of Israel: and I am the Lord your God, and there is none besides: and my people shall not be confounded for ever.
Sa’an nan za ku sani ina cikin Isra’ila, cewa ni ne Ubangiji Allahnku, babu wani kuma; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
28 And it shall come to pass after this, that I will pour out my spirit upon all flesh: and your sons and your daughters shall prophesy: your old men shall dream dreams, and your young men shall see visions.
“Daga baya kuma, zan zuba Ruhuna a bisan dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, tsofaffinku za su yi mafarkai, matasanku za su ga wahayoyi.
29 Moreover upon my servants and handmaids in those days I will pour forth my spirit.
Har ma a bisan bayina, maza da mata, zan zuba Ruhuna a kwanakin nan.
30 And I will shew wonders in heaven; and in earth, blood, and fire, and vapour of smoke.
Zan nuna abubuwan banmamaki a cikin sammai da kuma a kan duniya, za a ga jini da wuta da murtukewar hayaƙi.
31 The sun shall be turned into darkness, and the moon into blood: before the great and dreadful day of the Lord doth come.
Rana za tă duhunta wata kuma yă zama jini kafin isowar babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji.
32 And it shall come to pass, that every one that shall call upon the name of the Lord shall be saved: for in mount Sion, and in Jerusalem shall be salvation, as the Lord hath said, and in the residue whom the Lord shall call.
Amma dukan waɗanda suka nemi Ubangiji za su tsira. Kamar yadda Ubangiji ya ce, gama a Dutsen Sihiyona da Urushalima akwai ceto, a cikin waɗannan da Ubangiji ya kira.