< Job 6 >
1 But Job answered, and said:
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 O that my sins, whereby I have deserved wrath, and the calamity that I suffer, were weighed in a balance.
“Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
3 As the sand of the sea this would appear heavier: therefore my words are full of sorrow:
Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
4 For the arrows of the Lord are in me, the rage whereof drinketh up my spirit, and the terrors of the Lord war against me.
Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
5 Will the wild ass bray when he hath grass? or will the ox low when he standeth before a full manger?
Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
6 Or can an unsavoury thing be eaten, that is not seasoned with salt? or can a man taste that which when tasted bringeth death?
Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
7 The things which before my soul would not touch, now, through anguish are my meats.
Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
8 Who will grant that my request may come: and that God may give me what I look for?
“Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
9 And that he that hath begun may destroy me, that he may let loose his hand, and cut me off?
wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
10 And that this may be my comfort, that afflicting me with sorrow, he spare not, nor I contradict the words of the Holy One.
Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
11 For what is my strength, that I can hold out? or what is my end that I should keep patience?
“Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
12 My strength is not the strength of stones, nor is my flesh of brass.
Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
13 Behold there is no help for me in myself, and my familiar friends also are departed from me.
Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
14 He that taketh away mercy from his friend, forsaketh the fear of the Lord.
“Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
15 My brethren have passed by me, as the torrent that passeth swiftly in the valleys.
Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
16 They that fear the hoary frost, the snow shall fall upon them.
kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
17 At the time when they shall be scattered they shall perish: and after it groweth hot they shall be melted out of their place.
amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
18 The paths of their steps are entangled: they shall walk in vain, and shall perish.
Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
19 Consider the paths of Thema, the ways of Saba, and wait a little while.
Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
20 They are confounded, because I have hoped: they are come also even unto me, and are covered with shame.
Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
21 Now you are come: and now seeing my affliction you are afraid.
Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
22 Did I say: Bring to me, and give me of your substance?
Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
23 Or deliver me from the hand of the enemy, and rescue me out of the hand of the mighty?
ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
24 Teach me, and I will hold my peace: and if I have been ignorant in any thing, instruct me.
“Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
25 Why have you detracted the words of truth, whereas there is none of you that can reprove me?
Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
26 You dress up speeches only to rebuke, and you utter words to the wind.
Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
27 You rush in upon the fatherless, and you endeavour to overthrow your friend.
Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
28 However finish what you have begun, give ear, and see whether I lie.
“Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
29 Answer, I beseech you, without contention: and speaking that which is just, judge ye.
Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
30 And you shall not And iniquity in my tongue, neither shall folly sound in my mouth.
Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?