< Job 4 >
1 Then Eliphaz the Themanite answered, and said:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 If we begin to speak to thee, perhaps thou wilt take it ill, but who can withhold the words he hath conceived?
“In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
3 Behold thou hast taught many, and thou hast strengthened the weary hands:
Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
4 Thy words have confirmed them that were staggering, and thou hast strengthened the trembling knees:
Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
5 But now the scourge is come upon thee, and thou faintest: it hath touched thee, and thou art troubled.
Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
6 Where is thy fear, thy fortitude, thy patience, and the perfection of thy ways?
Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
7 Remember, I pray thee, who ever perished being innocent? or when were the just destroyed?
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8 On the contrary I have seen those who work iniquity, and sow sorrows, and reap them,
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9 Perishing by the blast of God, and consumed by the spirit of his wrath.
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
10 The roaring of the lion, and the voice of the lioness, and the teeth of the whelps of lions are broken:
Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
11 The tiger hath perished for want of prey, and the young lions are scattered abroad.
Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
12 Now there was a word spoken to me in private, and my ears by stealth as it were received the veins of its whisper.
“Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
13 In the horror of a vision by night, when deep sleep is wont to hold men,
Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
14 Fear seized upon me, and trembling, and all my bones were affrighted:
Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
15 And when a spirit passed before me, the hair of my flesh stood up.
Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
16 There stood one whose countenance I knew not, an image before my eyes, and I heard the voice as it were of a gentle wind:
Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
17 Shall man be justified in comparison of God, or shall a man be more pure than his maker?
‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
18 Behold they that serve him are not steadfast, and in his angels he found wickedness:
In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
19 How much more shall they that dwell in houses of clay, who have an earthly foundation, be consumed as with the moth?
to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
20 From morning till evening they shall be cut down: and because no one understandeth, they shall perish for ever.
Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
21 And they that shall be left, shall be taken away from them: they shall die, and not in wisdom.
Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’