< Job 30 >
1 But now the younger in time scorn me, whose fathers I would not have set with the dogs of my flock:
“Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
2 The strength of whose hands was to me as nothing, and they were thought unworthy of life itself.
Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
3 Barren with want and hunger, who gnawed in the wilderness, disfigured with calamity and misery.
Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
4 And they ate grass, and barks of trees, and the root of junipers was their food.
A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
5 Who snatched up these things out of the valleys, and when they had found any of them, they ran to them with a cry.
An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
6 They dwelt in the desert places of torrents, and in caves of earth, or upon the gravel.
An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
7 They pleased themselves among these kind of things, and counted it delightful to be under the briers.
Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
8 The children of foolish and base men, and not appearing at all upon the earth.
Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
9 Now I am turned into their song, and am become their byword.
“Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
10 They abhor me, and flee far from me, and are not afraid to spit in my face.
Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
11 For he hath opened his quiver, and hath afflicted me, and hath put a bridle into my mouth.
Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
12 At the right hand of my rising, my calamities forthwith arose: they have overthrown my feet, and have overwhelmed me with their paths as with waves.
A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
13 They have destroyed my ways, they have lain in wait against me, and they have prevailed, and there was none to help.
Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
14 They have rushed in upon me, as when a wall is broken, and a gate opened, and have rolled themselves down to my miseries.
Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
15 I am brought to nothing: as a wind thou hast taken away my desire: and my prosperity hath passed away like a cloud.
Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
16 And now my soul fadeth within myself, and the days of affliction possess me.
“Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
17 In the night my bone is pierced with sorrows: and they that feed upon me, do not sleep.
Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
18 With the multitude of them my garment is consumed, and they have girded me about, as with the collar of my coat.
A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
19 I am compared to dirt, and am likened to embers and ashes.
Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
20 I cry to thee, and thou hearest me not: I stand up, and thou dost not regard me.
“Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
21 Thou art changed to be cruel toward me, and in the hardness of thy hand thou art against me.
Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
22 Thou hast lifted me up, and set me as it were upon the wind, and thou hast mightily dashed me.
Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
23 I know that thou wilt deliver me to death, where a house is appointed for every one that liveth.
Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
24 But yet thou stretchest not forth thy hand to their consumption: and if they shall fall down thou wilt save.
“Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
25 I wept heretofore for him that was afflicted, and my soul had compassion on the poor.
Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
26 I expected good things, and evils are come upon me: I waited for light, and darkness broke out.
Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
27 My inner parts have boiled without any rest, the days of affliction have prevented me.
Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
28 I went mourning without indignation; I rose up, and cried in the crowd.
Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
29 I was the brother of dragons, and companion of ostriches.
Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
30 My skin is become black upon me, and my bones are dried up with heat.
Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
31 My harp is turned to mourning, and my organ into the voice of those that weep.
Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.