< Job 28 >
1 Silver hath beginnings of its veins, and gold hath a place wherein it is melted.
Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
2 Iron is taken out of the earth, and stone melted with heat is turned into brass.
Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
3 He hath set a time for darkness, and the end of all things he considereth, the stone also that is in the dark and the shadow of death.
Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
4 The flood divideth from the people that are on their journey, those whom the food of the needy man hath forgotten, and who cannot be come at.
Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
5 The land, out of which bread grew in its place, hath been overturned with fire.
Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
6 The stones of it are the place of sapphires, and the clods of it are gold.
akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
7 The bird hath not known the path, neither hath the eye of the vulture beheld it.
Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
8 The children of the merchants have not trodden it, neither hath the lioness passed by it.
Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
9 He hath stretched forth his hand to the flint, he hath overturned mountains from the roots.
Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
10 In the rocks he hath cut out rivers, and his eye hath seen every precious thing.
Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
11 The depths also of rivers he hath searched, and hidden things he hath brought forth to light.
Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
12 But where is wisdom to be found, and where is the place of understanding?
Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
13 Man knoweth not the price thereof, neither is it found in the land of them that live in delights.
Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
14 The depth saith: It is not in me: and the sea saith: It is not with me.
Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
15 The finest gold shall not purchase it, neither shall silver be weighed in exchange for it.
Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
16 It shall not be compared with the dyed colours of India, or with the most precious stone sardonyx, or the sapphire.
Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
17 Gold or crystal cannot equal it, neither shall any vessels of gold be changed for it.
Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
18 High and eminent things shall not be mentioned in comparison of it: but wisdom is drawn out of secret places.
Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
19 The topaz of Ethiopia shall not be equal to it, neither shall it be compared to the cleanest dyeing.
Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
20 Whence then cometh wisdom? and where is the place of understanding?
“To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
21 It is hid from the eyes of all living. and the fowls of the air know it not.
An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
22 Destruction and death have said: With our ears we have heard the fame thereof.
Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
23 God understandeth the way of it, and he knoweth the place thereof.
Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
24 For he beholdeth the ends of the world: and looketh on all things that are under heaven.
Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
25 Who made a weight for the winds and weighed the waters by measure.
Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
26 When he gave a law for the rain, and a way for the sounding storms.
Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
27 Then he saw it, and declared, and prepared, and searched it.
sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
28 And he said to man: Behold the fear of the Lord, that is wisdom: and to depart from evil, is understanding.
Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”