< Job 26 >
1 Then Job answered, and said:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Whose helper art thou? is it of him that is weak? and dost thou hold up the arm of him that has no strength?
“Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
3 To whom hast thou given counsel? perhaps to him that hath no wisdom, and thou hast shewn thy very great prudence.
Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
4 Whom hast thou desired to teach? was it not him that made life?
Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
5 Behold the giants groan under the waters, and they that dwell with them.
“Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
6 Hell is naked before him, and there is no covering for destruction. (Sheol )
Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol )
7 He stretched out the north over the empty space, and hangeth the earth upon nothing.
Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
8 He bindeth up the waters in his clouds, so that they break not out and fall down together.
Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
9 He withholdeth the face of his throne, and spreadeth his cloud over it.
Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
10 He hath set bounds about the waters, till light and darkness come to an end.
ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
11 The pillars of heaven tremble, and dread at his beck.
Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
12 By his power the seas are suddenly gathered together, and his wisdom has struck the proud one.
Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
13 His spirit hath adorned the heavens, and his obstetric hand brought forth the winding serpent.
Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
14 Lo, these things are said in part of his ways: and seeing we have heard scarce a little drop of his word, who shall be able to behold the thunder of his greatness?
Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”