< Job 22 >

1 Then Eliphaz the Themanite answered, and said:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 Can man be compared with God, even though he were of perfect knowledge?
“Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
3 What doth it profit God if thou be just? or what dost thou give him if thy way be unspotted?
Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
4 Shall he reprove thee for fear, and come with thee into judgment:
“Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
5 And not for thy manifold wickedness, and thy infinite iniquities?
Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
6 For thou hast taken away the pledge of thy brethren without cause, and stripped the naked of their clothing.
Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
7 Thou hast not given water to the weary, thou hast withdrawn bread from the hungry.
Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
8 In the strength of thy arm thou didst possess the land, and being the most mighty thou holdest it.
Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
9 Thou hast sent widows away empty, and the arms of the fatherless thou hast broken in pieces.
Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
10 Therefore art thou surrounded with snares, and sudden fear troubleth thee.
Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
11 And didst thou think that thou shouldst not see darkness, and that thou shouldst not be covered with the violence of overflowing waters?
An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
12 Dost not thou think that God is higher than heaven, and is elevated above the height of the stars?
“Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
13 And thou sayst: What doth God know? and he judgeth as it were through a mist.
Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
14 The clouds are his covert, and he doth not consider our things, and he walketh about the poles of heaven.
Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
15 Dost thou desire to keep the path of ages, which wicked men have trodden?
Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
16 Who were taken away before their time, and a flood hath overthrown their foundation.
An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
17 Who said to God: Depart from us: and looked upon the Almighty as if he could do nothing:
Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
18 Whereas he had filled their houses with good things: whose way of thinking be far from me.
Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
19 The just shall see, and shall rejoice, and the innocent shall laugh them to scorn.
“Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
20 Is not their exaltation cut down, and hath not fire devoured the remnants of them?
‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
21 Submit thyself then to him, and be at peace: and thereby thou shalt have the best fruits.
“Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
22 Receive the law of his mouth, and lay up his words in thy heart.
Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
23 If thou wilt return to the Almighty, thou shalt be built up, and shalt put away iniquity far from thy tabernacle.
In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
24 He shall give for earth flint, and for flint torrents of gold.
Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
25 And the Almighty shall be against thy enemies, and silver shall be heaped together for thee.
sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
26 Then shalt thou abound in delights in the Almighty, and shalt lift up thy face to God.
Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
27 Thou shalt pray to him, and he will hear thee, and thou shalt pay vows.
Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
28 Thou shalt decree a thing, and it I shall come to thee, and light shall shine in thy ways.
Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
29 For he that hath been humbled, shall be in glory: and he that shall bow down his eyes, he shall be saved.
Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
30 The innocent shall be saved, and he shall be saved by the cleanness of his hands.
Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”

< Job 22 >