< Job 19 >

1 Then Job answered, and said:
Sai Ayuba ya amsa,
2 How long do you afflict my soul, and break me in pieces with words?
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 Behold, these ten times you confound me, and are not ashamed to oppress me.
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 For if I have been ignorant, my ignorance shall be with me.
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 But you have set yourselves up against me, and reprove me with my reproaches.
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 At least now understand, that God hath not afflicted me with an equal judgment, and compassed me with his scourges.
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 Behold I cry suffering violence, and no one will hear: I shall cry aloud, and there is none to judge.
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 He hath hedged in my path round about, and I cannot pass, and in my way he hath set darkness.
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 He hath stripped me of my glory, and hath taken the crown from my head.
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 He hath destroyed me on every side, and I am lost, and he hath taken away my hope, as from a tree that is plucked up.
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 His wrath is kindled against me, and he hath counted me as his enemy.
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 His troops have come together, and have made themselves a way by me, and have besieged my tabernacle round about.
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 He hath put my brethren far from me, and my acquaintance like strangers have departed from me.
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 My kinsmen have forsaken me, and they that knew me, have forgotten me.
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 They that dwelt in my house, and my maidservants have counted me a stranger, and I have been like an alien in their eyes.
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 I called my servant, and he gave me no answer, I entreated him with my own mouth.
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 My wife hath abhorred my breath, and I entreated the children of my womb.
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 Even fools despise me; and when I gone from them, they spoke against me.
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 They that were sometime my counsellors, have abhorred me: and he whom I love most is turned against me.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 The flesh being consumed. My bone hath cleaved to my skin, and nothing but lips are left about my teeth.
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 Have pity on me, have pity on me, at least you my friends, because the hand of the Lord hath touched me.
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 Why do you persecute me as God, and glut yourselves with my flesh?
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 Who will grant me that my words may be written? Who will grant me that they may be marked down in a book?
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 With an iron pen and in a plate of lead, or else be graven with an instrument in flint stone.
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 For I know that my Redeemer liveth, and in the last day I shall rise out of the earth.
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 And I shall be clothed again with my skin, and in my flesh I will see my God.
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 Whom I myself shall see, and my eyes shall behold, and not another: this my hope is laid up in my bosom.
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 Why then do you say now: Let us persecute him, and let us find occasion of word against him?
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 Flee then from the face of the sword, for the sword is the revenger of iniquities: and know ye that there is judgment.
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”

< Job 19 >