< Job 18 >
1 Then Baldad the Suhite answered, and said:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 How long will you throw out words? understand first, and so let us speak.
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3 Why are we reputed as beasts, and counted vile before you?
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4 Thou that destroyest thy soul in thy fury, shall the earth be forsaken for thee, and shall rocks be removed out of their place?
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
5 Shall not the light of the wicked be extinguished, and the flame of his fire not shine?
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6 The light shall be dark in his tabernacle, and the lamp that is over him, shall be put out.
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7 The step of his strength shall be straitened, and his own counsel shall cast him down headlong.
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8 For he hath thrust his feet into a net, and walketh in its meshes.
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9 The sole of his foot shall be held in a snare, and thirst shall burn against him.
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10 A gin is hidden for him in the earth, and his trap upon the path.
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
11 Fears shall terrify him on every side, and shall entangle his feet.
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12 Let his strength be wasted with famine, and let hunger invade his ribs.
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13 Let it devour the beauty of his skin, let the firstborn death consume his arms.
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14 Let his confidence be rooted out of his tabernacle, and let destruction tread upon him like a king.
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
15 Let the companions of him that is not, dwell in his tabernacle, let brimstone be sprinkled in his tent.
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16 Let his roots be dried up beneath, and his harvest destroyed above.
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17 Let the memory of him perish from the earth and let not his name be renowned in the streets.
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18 He shall drive him out of light into darkness, and shall remove him out of the world.
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19 His seed shall not subsist, nor his offspring among his people, nor any remnants in his country.
Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20 They that come after him shall be astonished at his day, and horror shall fall upon them that went before.
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21 These men are the tabernacles of the wicked, and this the place of him that knoweth not God.
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”