< Job 13 >
1 Behold my eye hath seen all these things, and my ear hath heard them, and I have understood them all.
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
2 According to your knowledge I also know: neither am I inferior to you.
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
3 But yet I will speak to the Almighty, and I desire to reason with God.
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
4 Having first shewn that you are forgers of lies, and maintainers of perverse opinions.
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
5 And I wish you would hold your peace, that you might be thought to be wise men.
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
6 Hear ye therefore my reproof, and attend to the judgment of my lips.
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7 Hath God any need of your lie, that you should speak deceitfully for him?
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8 Do you accept his person, and do you endeavour to judge for God?
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9 Or shall it please him, from whom nothing can be concealed? or shall he be deceived as a man, with your deceitful dealings?
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10 He shall reprove you, because in secret you accept his person.
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11 As soon as he shall move himself, he shall trouble you: and his dread shall fall upon you.
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12 Your remembrance shall be compared to ashes, and your necks shall be brought to clay.
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
13 Hold your peace a little while, that I may speak whatsoever my mind shall suggest to me.
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
14 Why do I tear my flesh with my teeth, and carry my soul in my hands?
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
15 Although he should bill me, I will trust in him: but yet I will reprove my ways in his sight.
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
16 And he shall be my saviour: for no hypocrite shall come before his presence.
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
17 Hear ye my speech, and receive with Sour ears hidden truths.
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
18 If I shall be judged, I know that I shall be found just.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
19 Who is he that will plead against me? let him come: why am I consumed holding my peace?
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
20 Two things only do not to me, and then from thy face I shall not be hid:
“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
21 Withdraw thy hand far from me, and let not thy dread terrify me.
Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
22 Call me, and I will answer thee: or else I will speak, and do thou answer me.
Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
23 How many are my iniquities and sins? make me know my crimes and offences.
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
24 Why hidest thou thy face, and thinkest me thy enemy?
Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
25 Against a leaf, that is carried away with the wind, thou shewest thy power, and thou pursuest a dry straw.
Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
26 For thou writest bitter things against me, and wilt consume me for the sins of my youth.
Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
27 Thou hast put my feet in the stocks, and hast observed all my paths, and hast considered the steps of my feet:
Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
28 Who am to be consumed as rottenness, and as a garment that is moth-eaten.
“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.