< Job 12 >
1 When Job answered, and said:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Are you then men alone, and shall wisdom die with you?
“Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
3 I also have a heart as well as you: for who is ignorant of these things, which you know?
Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
4 He that is mocked by his friends as I, shall call upon God and he will hear him: for the simplicity of the just man is laughed to scorn.
“Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
5 The lamp despised in the thoughts of the rich, is ready for the time appointed.
Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
6 The tabernacles of robbers abound, and they provoke God boldly; whereas it is he that hath given all into their hands:
Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
7 But ask now the beasts, and they shall teach thee: and the birds of the air, and they shall tell thee.
“Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
8 Speak to the earth, and it shall answer thee: and the fishes of the sea shall tell.
Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
9 Who is ignorant that the hand of the Lord hath made all these things?
Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
10 In whose hand is the soul of every living thing, and the spirit of all flesh of man.
Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
11 Doth not the ear discern words, and the palate of him that eateth, the taste?
Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
12 In the ancient is wisdom, and in length of days prudence.
Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
13 With him is wisdom and strength, he hath counsel and understanding.
“Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
14 If he pull down, there is no man that can build up: if he shut up a. man, there is none that can open.
Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
15 If he withhold the waters, all things shall be dried up: and if he send them out, they shall overturn the earth.
Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
16 With him is strength and wisdom: he knoweth both the deceiver, and him that is deceived.
Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
17 He bringeth counsellors to a foolish end, and judges to insensibility.
Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
18 He looseth the belt of kings, and girdeth their loins with a cord.
Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
19 He leadeth away priests without glory, and overthroweth nobles.
Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
20 He changeth the speech of the true speakers, and taketh away the doctrine of the aged.
Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
21 He poureth contempt upon princes, and relieveth them that were oppressed.
Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
22 He discovereth deep things out of darkness, and bringeth up to light the shadow of death.
Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
23 He multiplieth nations, and destroyeth them, and restoreth them again after they were overthrown.
yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
24 He changeth the heart of the princes of the people of the earth, and deceiveth them that they walk in vain where there is no way.
Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
25 They shall grope as in the dark, and not in the light, and he shall make them stagger like men that are drunk.
Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.