< Job 11 >

1 Then Sophar the Naamathite answered, and said:
Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 Shall not he that speaketh much, hear also? or shall a man full of talk be justified?
“Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
3 Shall men hold their peace to thee only? and when thou hast mocked others, shall no man confute thee?
Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
4 For thou hast said: My word is pure, and I am clean in thy sight.
Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
5 And I wish that God would speak with thee, and would open his lips to thee,
Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
6 That he might shew thee the secrets of wisdom, and that his law is manifold, and thou mightest understand that he exacteth much less of thee, than thy iniquity deserveth.
yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
7 Peradventure thou wilt comprehend the steps of God, and wilt find out the Almighty perfectly?
“Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
8 He is higher than heaven, and what wilt thou do? he is deeper than hell, and how wilt thou know? (Sheol h7585)
Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
9 The measure of him is longer than the earth, and broader than the sea.
Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
10 If he shall overturn all things, or shall press them together, who shall contradict him?
“In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
11 For he knoweth the vanity of men, and when he seeth iniquity, doth he not consider it?
Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
12 A vain man is lifted up into pride, and thinketh himself born free like a wild ass’s colt.
Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
13 Rut thou hast hardened thy heart, and hast spread thy hands to him.
“Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
14 If thou wilt put away from thee the iniquity that is in thy hand, and lot not injustice remain in thy tabernacle:
in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
15 Then mayst thou lift up thy face without spot, and thou shalt be steadfast, and shalt not fear.
shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
16 Thou shalt also forget misery, and remember it only as waters that are passed away.
Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
17 And brightness like that of the noonday, shall arise to thee at evening: and when thou shalt think thyself consumed, thou shalt rise as the day star.
Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
18 And thou shalt have confidence, hope being set before thee, and being buried thou shalt sleep secure.
Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
19 Thou shalt rest, and there shall be none to make thee afraid: and many shall entreat thy face.
Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
20 But the eyes of the wicked shall decay, and the way to escape shall fail them, and their hope the abomination of the soul.
Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”

< Job 11 >