< Jeremiah 7 >
1 The word that came to Jeremias from the Lord, saying:
Maganar da ta zo wa Irmiya ke nan daga Ubangiji.
2 Stand in the gate of the house of the Lord, and proclaim there this word, and say: Hear ye the word of the Lord, all ye men of Juda, that enter in at these gates, to adore the Lord.
“Ka tsaya a ƙofar gidan Ubangiji, a can kuwa ka yi shelar wannan saƙo. “‘Ku ji maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi don yin sujada ga Ubangiji.
3 Thus saith the Lord of hosts the God of Israel: Make your ways and your doings good: and I will dwell with you in this place.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allahna Isra’ila, yana cewa ku gyara hanyoyinku da ayyukanku, zan kuwa bar ku ku zauna a wannan wuri.
4 Trust not in lying words, saying: The temple of the Lord, the temple of the Lord, it is the temple of the Lord.
Kada ku dogara ga maganganun nan na ruɗarwa cewa, “Wannan shi ne haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji!”
5 For if you will order well your ways, and your doings: if you will execute judgement between a man and his neighbor,
In dai kuka canja hanyoyinku da ayyukanku kuma kuna aikata adalci da junanku,
6 If you opress not the stranger, the fatherless, and the widow, and shed not innocent blood in this place, and walk not after strange gods to your own hurt,
in ba ku zalunci baƙo, maraya ko gwauruwa ba kuma in ba ku zub da jinin marar laifi a wannan wuri ba, in kuma ba ku bi waɗansu alloli da za su cuce ku ba,
7 I will dwell with you in this place: in the land, which I gave to your fathers from the beginning and for evermore.
to, zan bar ku ku zauna a wannan wuri, a ƙasar da na ba kakanninku har abada abadin.
8 Behold you put your trust in lying words, which shall not profit you:
Amma ga shi, kuna dogara ga maganganu na ruɗami marasa amfani.
9 To steal, to murder, to commit adultery, to swear falsely, to offer to Baalim, and to go after strange gods, which you know not.
“‘Za ku yi sata da kisa, ku yi zina da rantsuwar ƙarya, kuna ƙone turare wa Ba’al kuna kuma bin waɗansu allolin da ba ku sani ba,
10 And you have come, and stood before me in this house, in which my name is called upon, and have said: We are delivered, because we have done all these abominations.
sa’an nan ku zo ku tsaya a gabana a wannan gida, wanda ake kira da Sunana, kuna cewa, “An cece mu,” mun dace mu aikata waɗannan abubuwa banƙyama?
11 Is this house then, in which my name hath been called upon, in your eyes become a den of robbers? I, I am he: I have seen it, saith the Lord.
Wannan gidan da ake kira da Sunana ya zama kogon’yan fashi ne a gare ku? Amma ina kallo! In ji Ubangiji.
12 Go ye to my place in Silo, where my name dwelt from the beginning: and see what I did to it for the wickedness of my people Israel:
“‘Yanzu ku fita zuwa Shilo inda na fara maishe shi wurin zama don Sunana, ku ga abin da na yi masa saboda muguntar mutanen Isra’ila.
13 And now, because you have done all these works, saith the Lord: and I have spoken to you rising up early, and speaking, and you have not heard: and I have called you, and you have not answered:
Yayinda kuke yin dukan waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji, na yi muku magana sau da sau, amma ba ku ji ba; na kira ku, amma ba ku amsa ba.
14 I will do to this house, in which my name is called upon, and in which you trust, and to the places which I have given you and your fathers, as I did to Silo.
Saboda haka, abin da na yi wa Shilo shi ne yanzu zan yi wa gidan da ake kira da Sunana, haikalin da kuka dogara a kai, wurin da na ba ku da kuma kakanninku.
15 And I will cast you away from before my face, as I have cast away all your brethren, the whole seed of Ephraim.
Zan kore ku daga gabana, kamar yadda na yi ga dukan’yan’uwanku, mutanen Efraim.’
16 Therefore, do not thou pray for this people, nor take to thee praise and supplication for them: and do not withstand me: for I will not hear thee.
“Saboda haka kada ka yi addu’a don wannan mutane ko ka yi wani kuka ko roƙo dominsu, gama ba zan ji ka ba.
17 Seest thou not what they do in the cities of Juda, and in the streets of Jerusalem?
Ba ka gani abin da suke yi a biranen Yahuda da kuma a titunan Urushalima?
18 The children gather wood, and the fathers kindle the fire and the women knead the dough, to make cakes to the queen of heaven, and to offer libations to strange gods, and to provoke me to anger.
Yara sukan tara itace, iyaye suka hura wuta, mata kuma sukan kwaɓa kullu don su yi wa Sarauniyar Sama waina. Sukan miƙa hadayun sha ga waɗansu alloli don su tsokane ni in yi fushi.
19 Do they provoke me to anger, saith the Lord? Is it not themselves, to the confusion of their contenance?
Amma ni ne suke tsokana? In ji Ubangiji Ashe, ba kansu ne suke cuta, suna kunyata kansu ba?
20 Therefore thus saith the Lord God: Behold my wrath and my indignation was enkindled against this place, upon men and upon beasts, and upon the trees of the field, and upon the fruits of the land, and it shall burn, and shall not be quenched.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa fushina da hasalata za su kwarara a wannan wuri, a kan mutum da dabba, a kan itatuwan fili da a kan amfanin gona, za su yi ta kuna, ba kuwa za a kashe ba.
21 Thus saith the Lord of hosts the God of Israel: Add your burnt offerings to your sacrifices, and eat ye the flesh.
“‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa ci gaba, ku ƙara hadayun ƙonawarku da sauran sadakoki ku kuma yi ta cin naman!
22 For I spoke not to your fathers, and I commanded them not, in the day that I brought them out of the land of Egypt, concerning the matter of burnt offerings and sacrifices.
Gama sa’ad da na fitar da kakanninku daga Masar na kuma yi musu magana, ban ba su dokoki kawai game da hadayun ƙonawa da sadakoki ba,
23 But this thing I commanded them, saying: Hearken to my voice, and I will be your God, and you shall be my people: and walk ye in all the way that I have commanded you, that it may be well with you.
amma na ba su wannan umarni cewa ku yi mini biyayya, zan kuwa zama Allahnku ku kuma ku zama mutanena. Ku yi tafiya cikin dukan hanyoyin da na umarce ku, don ku zauna lafiya.
24 But they hearkened not, nor inclined their ear: but walked in their own will, and in the perversity of their wicked heart: and went backward and not forward,
Amma ba su saurara ba, ba su kuwa kula ba; a maimako, suka bi shawarar kansu da ta taurare muguwar zukatansu. Su ja da baya a maimakon yin gaba.
25 From the day that their fathers came out of the land of Egypt, even to this day. And I have sent to you all my servants the prophets from day to day, rising up early and sending.
Daga lokacin da kakanninku suka bar Masar har yă zuwa yau, kullum na yi ta aikan bayina annabawa.
26 And they have not hearkened to me: nor inclined their ear: but have hardened their neck, and have done worse than their fathers.
Amma ba su saurare ni ba, ba su kula ba. Sai suka taurare zukatansu suka aikata mugun abu fiye da na kakanninsu.’
27 And thou shalt speak to them all these words, but they will not hearken to thee: and thou shalt call them, but they will not answer thee.
“Sa’ad da ka faɗa musu wannan duka, ba za su saurare ka ba; sa’ad da ka kira su, ba za su amsa ba.
28 And thou shalt say to them: This is a nation which hath not hearkened to the voice of the Lord their God, nor received instruction: Faith is lost, and is carried away out of their mouth.
Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Wannan ce al’ummar da ba tă yi biyayya ga Ubangiji Allahnta ba, ba kuwa ta karɓi gyara ba. Gaskiya ta ƙare; ta ɓace gaba ɗaya daga leɓunansu.
29 Cut off thy hair, and cast it away: and take up a lamentation on high: for the Lord hath rejected and forsaken the generation of his wrath,
“‘Ku aske gashin kanku ku zubar; ku yi makoki a filayen tuddai, gama Ubangiji ya ƙi’yan zamanin nan ya kuma rabu da su saboda fushin da suka ba shi.
30 Because the children of Juda have done evil in my eyes, saith the Lord. They have set their abominations in the house in which my name is called upon, to pollute it;
“‘Mutanen Yahuda sun yi mugunta a gabana, in ji Ubangiji. Sun kafa gumakansu masu banƙyama a gidan da ake kira da Sunana suka ƙazantar da shi.
31 And they have built the high places of Topeth, which is in the valley of the son of Ennom, to burn their sons, and their daughters in the fire: which I commanded not, nor thought on in my heart.
Sun gida masujadan Tofet a Kwarin Ben Hinnom don miƙa’ya’yansu maza da mata a wuta, abin da ban yi umarni ba, ba kuwa yi tunaninsa ba.
32 Therefore behold the days shall come, saith the Lord, and it shall no more be called Topeth, nor the valley of the son of Ennom: but the valley of slaughter, and they shall bury in Topeth, because there is no place.
Saboda haka ku yi hankali, kwanaki suna zuwa in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara kira wurin Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma Kwarin Kisa, gama za su binne matattu a Tofet sai har ba sauran wuri.
33 And the carcasses of this people shall be meat for the fowls of the air, and for the beasts of the earth, and there shall be non to drive them away.
Sa’an nan gawawwakin wannan mutane za su zama abinci ga tsuntsayen sama da kuma namun jeji, ba za a kuwa sami wani da zai kore su ba.
34 And I will cause to cease out of the cities of Juda, and out of the streets of Jerusalem, the voice of joy, and the voice of gladness, the voice of the bridegroom and the voice of the bride: for the land shall be desolate.
Zan kawo ƙarshen muryar murna da farin ciki da muryar amarya da ango a garuruwan Yahuda da kuma a titunan Urushalima, gama ƙasar za tă zama kufai.