< Jeremiah 36 >

1 And it came to pass in the fourth year of Joakim the son of Josias king of Juda, that this word came to Jeremias by the Lord, saying:
A shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
2 Take thee a roll of a book, and thou shalt write in it all the words that I have spoken to thee against Israel and Juda, and against all the nations from the day that I spoke to thee, from the days of Josias even to this day.
“Ka ɗauki littafi ka rubuta dukan maganganun da na yi maka game da Isra’ila, Yahuda da kuma dukan sauran al’ummai daga lokacin da na fara maka magana a mulkin Yosiya har zuwa yanzu.
3 If so be, when the house of Juda shall hear all the evils that I purpose to do unto them, that they may return every man from his wicked way: and I will forgive their iniquity, and their sin.
Wataƙila sa’ad da mutanen Yahuda suka ji game da kowace masifar da na shirya in auka musu, kowa ya juya daga muguwar hanyarsa; sa’an nan in gafarta musu muguntarsu da kuma zunubinsu.”
4 So Jeremias called Baruch the son of Nerias: and Baruch wrote from the mouth of Jeremias all the words of the Lord, which he spoke to him, upon the roll of a book.
Saboda haka Irmiya ya kira Baruk ɗan Neriya, yayinda Irmiya yake fadar dukan waɗannan maganganun da Ubangiji ya faɗa masa, Baruk ya rubuta su a littafin.
5 And Jeremias commanded Baruch, saying: I am shut up, and cannot go into the house of the Lord.
Sai Irmiya ya ce wa Baruk, “An hana ni, ba zan tafi haikalin Ubangiji ba.
6 Go thou in therefore, and read out of the volume, which thou hast written from my mouth, the words of the Lord, in the hearing of all the people in the house of the Lord on the fasting day: and also thou shalt read them in the hearing of all Juda that come out of their cities:
Saboda haka ka tafi gidan Ubangiji a ranar azumi ka karanta wa mutane daga littafin maganar Ubangiji da na shibta maka ka rubuta. Ka karanta su ga dukan mutanen Yahuda waɗanda suka zo daga garuruwansu.
7 If so be they may present their supplication before the Lord, and may return every one from his wicked way: for great is the wrath and indignation which the Lord hath pronounced against this people.
Wataƙila za su kawo kukansu a gaban Ubangiji, kowanne kuma ya juya daga muguwar hanyarsa, gama fushi da hasalar da Ubangiji ya furta a kan mutanen nan yana da girma.”
8 And Baruch the son of Nerias did according to all that Jeremias the prophet had commanded him, reading out of the volume the words of the Lord in the house of the Lord.
Sai Baruk ɗan Neriya ya yi dukan abin da annabi Irmiya ya ce ya yi; a haikalin Ubangiji kuwa ya karanta maganar Ubangiji daga littafin
9 And it came to pass in the fifth year of Joakim the son of Josias king of Juda, in the ninth month, that they proclaimed a fast before the Lord to all the people in Jerusalem, and to all the people that were come together out of the cities of Juda to Jerusalem.
A watan tara na shekara ta biyar ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, an yi shela a yi azumi a gaban Ubangiji ga dukan mutanen Urushalima da waɗanda suka zo daga garuruwan Yahuda.
10 And Baruch read out of the volume the words of Jeremias in the house of the Lord, in the treasury of Gamarias the son of Saphan the scribe, in the upper court, in the entry of the new gate of the house of the Lord, in the hearing of all the people.
Daga ɗakin Gemariya ɗan Shafan magatakarda, wanda yake a fili na bisa a mashigin Sabuwar Ƙofar haikali, Baruk ya karanta wa dukan mutane a haikalin Ubangiji maganar Irmiya daga littafin.
11 And when Micheas the son of Gamarias the son of Saphan had heard out of the book all the words of the Lord,
Sa’ad da Mikahiya ɗan Gemariya, ɗan Shafan, ya ji dukan maganar Ubangiji daga littafin,
12 He went down into the king’s house to the secretary’s chamber: and behold all the princes sat there, Elisama the scribe, and Dalaias the son of Semeias, and Elnathan the son of Achobor, and Gamarias the son of Saphan, and Sedecias the son of Hananias, and all the princes.
sai ya sauka zuwa ɗakin magatakarda a fada, inda dukan fadawa suke zaune, Elishama magatakarda, Delahiya ɗan Shemahiya, Elnatan ɗan Akbor, Gemariya ɗan Shafan, Zedekiya ɗan Hananiya, da dukan sauran fadawa.
13 And Micheas told them all the words that he had heard when Baruch read out of the volume in the hearing of the people.
Bayan Mikahiya ya faɗa musu kome da ya ji Baruk ya karanta wa mutane daga littafin,
14 Therefore all the princes sent Judi the son of Nathanias, the son of Selemias, the son of Chusi, to Baruch, saying: Take in thy hand the volume in which thou hast read in the hearing of the people, and come. So Baruch the son of Nerias took the volume in his hand, and came to them.
sai dukan fadawan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya ce wa Baruk, “Ka zo tare da littafin da ka karanta wa mutane.” Saboda haka Baruk ɗan Neriya ya tafi wurinsu tare da littafin a hannunsa.
15 And they said to him: Sit down and read these things in our hearing. And Baruch read in their hearing.
Suka ce masa, “Zauna, ka karanta mana littafin.” Sai Baruk ya karanta musu littafin.
16 And when they had heard all the words, they looked upon one another with astonishment, and they said to Baruch: We must tell the king all these words.
Da suka ji dukan maganar, sai suka dubi juna a firgice suka ce wa Baruk, “Dole mu sanar da dukan maganan nan ga sarki.”
17 And they asked him, saying: Tell us how didst thou write all these words from his mouth.
Sa’an nan suka ce wa Baruk, “Faɗa mana yadda ka yi ka rubuta dukan wannan. Irmiya ne ya yi maka shibtar ta?”
18 And Baruch said to them: With his mouth he pronounced all these words as if he were reading to me: and I wrote in a volume with ink.
Baruk ya amsa ya ce, “I, shi ne ya faɗa mini dukan wannan magana, na kuwa rubuta su a takarda.”
19 And the princes said to Baruch: Go, and hide thee, both thou and Jeremias, and let no man know where you are.
Sa’an nan fadawan suka ce wa Baruk, “Kai da Irmiya ku je ku ɓuya. Kada ku bari wani ya san inda kuke.”
20 And they went in to the king into the court: but they laid up the volume in the chamber of Elisama the scribe: and they told all the words in the hearing of the king.
Bayan da suka ajiye littafin a ɗakin Elishama magatakarda, sai suka tafi wurin sarki a fili suka sanar da shi kome.
21 And the king sent Judi that he should take the volume: who bringing it out of the chamber of Elisama the scribe, read it in the hearing of the king, and of all the princes that stood about the king.
Sai sarki ya aiki Yehudi ya kawo littafin daga ɗakin Elishama magatakarda ya kuma karanta wa sarki da kuma dukan fadawan da suke tsaye kusa da shi.
22 Now the king sat in the winter house, In the ninth month: and there was a hearth before him full of burning coals.
A watan tara ne sarki kuwa yana zaune a gidansa na rani, wuta kuwa tana ci a kasko a gabansa.
23 And when Judi had read three or four pages, he cut it with the penknife, and he cast it into the Are, that was upon the hearth, till all the volume was consumed with the fire that was on the hearth.
Duk sa’ad da Yehudi ya karanta sashi uku ko huɗu na littafin, sai sarkin ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da take ci a kasko, da haka ya ƙone dukan littafin.
24 And the king and all his servants that heard all these words were not afraid, nor did they rend their garments.
Sai sarki da dukan masu yin masa hidima waɗanda suke jin maganan nan ba su firgita ba, balle su keta rigunansu.
25 But yet Elnathan, and Dalaias, and Gamarias spoke to the king, not to burn. the book: and he heard them not.
Ko da yake Elnatan, Delahiya da Gemariya sun roƙi sarki kada yă ƙone littafin, bai saurare su ba.
26 And the king commanded Jeremiel the son of Amelech, and Saraias the son of Ezriel, and Selemias the son of Abdeel, to take up Baruch the scribe, and Jeremias the prophet: but the Lord hid them.
A maimakon haka, sai sarki ya umarci Yerameyel ɗan sarki, Serahiya ɗan Azriyel da Shelemiya ɗan Abdeyel su kama Baruk marubuci da Irmiya annabi. Amma Ubangiji ya ɓoye su.
27 And the word of the Lord came to Jeremias the prophet, after that the king had burnt the volume, and the words that Baruch had written from the mouth of Jeremias, saying:
Bayan sarki ya ƙone littafin da ya ƙunshi maganar da Baruk ya rubuta daga shibtar Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
28 Take thee again another volume: and write in it all the former words that were in the first volume which Joakim the king of Juda hath burnt.
“Ka ɗauki wani littafi ka rubuta a kansa dukan maganar da littafi na farin ya ƙunsa, wanda Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone.
29 And thou shalt say to Joakim the king of Juda: Thus saith the Lord: Thou hast burnt that volume, saying: Why hast thou written therein, and said: The king of Babylon shall come speedily, and shall lay waste this land: and shall cause to cease from thence man and beast?
Ka kuma faɗa wa Yehohiyakim sarkin Yahuda cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka ƙone wancan littafin ka kuma ce, “Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle sarkin Babilon zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?”
30 Therefore thus saith the Lord against Joakim the king of Juda: He shall have none to sit upon the throne of David: and his dead body shall be cast out to the heat by day, and to the frost by night.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim sarkin Yahuda. Ba zai kasance da wani wanda zai zauna a kan gadon sarautar Dawuda ba; za a jefar da gawarsa ta sha zafi da rana da dare kuma ta sha matsanancin sanyi.
31 And I will punish him, and his seed and his servants, for their iniquities, and I will bring upon them, and upon the inhabitants of Jerusalem, and upon the men of Juda all the evil that I have pronounced against them, but they have not heard.
Zan hukunta shi da kuma’ya’yansa da masu hidimarsa saboda muguntarsu; zan kawo kowace masifar da na furta a kansu da kuma waɗanda suke zama a Urushalima da na Yahuda, domin sun ƙi su saurara.’”
32 And Jeremias took another volume, and gave it to Baruch the son of Nerias the scribe: who wrote in it from the mouth of Jeremias all the words of the book which Joakim the king of Juda had burnt with fire: and there were added besides many more words than had been before.
Sai Irmiya ta ɗauko wani littafi ya ba wa Baruk ɗan Neriya marubuci, kuma yayinda Irmiya yake shibtawa, Baruk ya rubuta a littafin dukan maganar da take a littafin da Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone. Ya kuma ƙara ire-iren maganganun nan a kansu.

< Jeremiah 36 >