< Jeremiah 3 >
1 It is commonly said: If a man put away his wife, and she go from him, and marry another man, shall he return to her any more? shall not that woman be polluted, and defiled? but thou hast prostituted thyself to many lovers: nevertheless return to me, saith the Lord, and I will receive thee.
“In mutum ya saki matarsa ta kuwa bar shi ta auri wani mutum, zai iya komo da ita kuma? Ƙasar ba za tă ƙazantu gaba ɗaya ba? Amma kun yi rayuwa kamar karuwa da masoya masu yawa yanzu za ki komo wurina?” In ji Ubangiji.
2 Lift up thy eyes on high: and see where thou hast not prostituted thyself: Thou didst sit in the ways, waiting for them as a robber in the wilderness: and thou hast polluted the land with thy fornications, and with thy wickedness.
“Ta da idanu ki duba tsaunuka ki gani. Akwai wani wurin da ba a kwana da ke ba? A gefen hanya kin zauna kina jiran masoyanki, kin zauna kamar makiyayi a hamada. Kin ƙazantar da ƙasar da karuwancinki da muguntarki.
3 Therefore the showers were withholden, and there was no lateward rain: thou hadst a harlot’s forehead, thou wouldst not blush.
Saboda haka an hana yayyafi, kuma babu ruwan bazara da ya sauka. Duk da haka kina da irin kallon da karuwa takan yi; kin ƙi ki ji kunya.
4 Therefore at least at this time call to me: Thou art my father, the guide of my virginity:
Yanzu ba kin kira ni, ‘Mahaifina, abokina daga ƙuruciyata ba,
5 Wilt thou be angry for ever, or wilt thou continue until the end? Behold, thou hast spoken, and hast done evil things, and hast been able.
kullum za ka riƙa fushi? Hasalarka za tă ci gaba har abada ne?’ Haka kike magana, amma kina aikata dukan muguntar da kika iya yi.”
6 And the Lord said to me in the days of king Josias: Hast thou seen what rebellious Israel hast done? she hath gone out of herself upon every high mountain, and under every green tree, and hath played the harlot there.
A zamanin Sarki Yosiya, Ubangiji ya ce mini, “Ka ga abin da marar amincin nan, Isra’ila ta yi? Ta haura kan kowane tudu mai tsayi da kowane gindin itace mai duhuwa ta yi zina a can.
7 And when she had done all these things, I said: Return to me, and she did not return. And her treacherous sister Juda saw,
Na yi zaton bayan ta yi wannan duka, za tă komo wurina amma ba tă yi haka ba,’yar’uwarta marar aminci nan Yahuda ta gani.
8 That because the rebellious Israel had played the harlot, I had put her away, and had given her a bill of divorce: yet her treacherous sister Juda was not afraid, but went and played the harlot also herself.
Na ba wa Isra’ila marar bangaskiya takardar saki na kuwa kore ta saboda duk zinanta. Duk da haka na ga cewa’yar’uwarta marar amincin nan Yahuda ba ta da tsoro; ita ma ta fita ta yi zina.
9 And by the facility of her fornication she defiled the land, and played the harlot with stones and with stocks.
Domin fasikancin Isra’ila bai yi tasiri gare ta ba, sai ta ƙazantar da ƙasar ta kuma yi zina da dutse da kuma itace.
10 And after all this, her treacherous sister Juda hath not returned to me with her whole heart, but with falsehood, saith the Lord.
Duk da wannan duka, Yahuda’yar’uwarta rashin amincin ba tă komo gare ni da dukan zuciyarta ba, sai a munafunce,” in ji Ubangiji.
11 And the Lord said to me: The rebellious Israel hath justified her soul, in comparison of the treacherous Juda.
Ubangiji ya ce mini, “Isra’ila marar bangaskiya ta fi Yahuda marar aminci.
12 Go, and proclaim these words toward the north, and thou shalt say: Return, O rebellious Israel, saith the Lord, and I will not turn away my face from you: for I am holy, saith the Lord, and I will not be angry for ever.
Ka tafi, ka yi shelar saƙon nan wajen arewa cewa, “‘Ki komo, Isra’ila marar bangaskiya,’ in ji Ubangiji, ‘Ba zan ƙara yin fushi da ke ba, gama ni mai jinƙai ne,’ in ji Ubangiji, ‘Ba zan yi fushi da ke har abada ba.
13 But yet acknowledge thy iniquity, that thou hast transgressed against the Lord thy God: and thou hast scattered thy ways to strangers under every green tree, and hast not heard my voice, saith the Lord.
Ki dai yarda da laifinki kin yi wa Ubangiji Allahnki tawaye, kin watsar da alheranki ga baƙin alloli a ƙarƙashin kowane itace mai duhuwa, ba ki kuwa yi mini biyayya ba,’” in ji Ubangiji.
14 Return, O ye revolting children, saith the Lord: for I am your husband: and I will take you, one of a city, and two of a kindred, and will bring you into Sion.
“Ku komo, ku mutane marasa bangaskiya,” in ji Ubangiji, “gama ni ne mijinku. Zan ɗauke ku, ɗaya daga garuruwanku da kuma biyu daga zuriyarku in kawo ku a Sihiyona.
15 And I will give you pastors according to my own heart, and they shall feed you with knowledge and doctrine.
Sa’an nan zan ba ku makiyaya da suke yin abin da zuciyata take so, waɗanda za su bishe ku da sani da kuma fahimi.
16 And when you shall be multiplied, and increase in the land in those days, saith the Lord, they shall say no more: The ark of the covenant of the Lord: neither shall it come upon the heart, neither shall they remember it, neither shall it be visited, neither shall that be done any more.
A kwanakin, sa’ad da kuka ƙaru sosai a ƙasar,” in ji Ubangiji, “mutane ba za su ƙara yin magana a kan, ‘Akwatin alkawarin Ubangiji ba.’ Ba zai ƙara shiga zuciyarsu ko su tuna ba; ko su bukace shi, ko kuwa su yi wani irinsa ba.
17 At that time Jerusalem shall be called the thrown of the Lord: and all the nations shall be gathered together to it, in the name of the Lord to Jerusalem, and they shall not walk after the perversity of their most wicked heart.
A lokacin za su ce da Urushalima Kursiyin Ubangiji, kuma dukan al’ummai za su taru a Urushalima don su girmama sunan Ubangiji. Ba za su ƙara bin taurinkai zuciyarsu mai mugunta ba.
18 In those days the house of Juda shall go to the house of Israel, and they shall come together out of the land of the north to the land which I gave to your fathers.
A kwanakin gidan Yahuda zai haɗu da gidan Isra’ila, tare kuma za su zo daga ƙasar da take wajen arewa zuwa ƙasar da na ba kakanninsu gādo.
19 But I said: How shall I put thee among the children, and give thee a lovely land, the goodly inheritance of the armies of the Gentiles? And I said: Thou shalt call me father and shalt cease to walk after me.
“Ni kaina na faɗa, “‘Da farin ciki zan ɗauke ki kamar’ya’yana maza in ba ki ƙasa mai daɗi, gādo mafi kyau da wata al’umma.’ Na zaci za ki kira ni ‘Mahaifi’ ba za ki ƙara rabuwa da bina ba.
20 But as a woman that despiseth her lover, so hath the house of Israel despised me, saith the Lord.
Amma kamar mace marar aminci ga mijinta, haka kika kasance marar aminci gare ni, ya gidan Isra’ila,” in ji Ubangiji.
21 A voice was heard in the highways, weeping and howling of the children of Israel: because they have made their way wicked, they have forgotten the Lord their God.
An ji kuka a filayen tuddai, kuka da roƙon mutanen Isra’ila, domin sun lalace hanyoyinsu sun kuma manta da Ubangiji Allahnsu.
22 Return, you rebellious children, and I will heal your rebellions. Behold we come to thee: for thou art the Lord our God.
“Ku komo, mutane marasa bangaskiya; zan warkar da ku daga ja da bayanku.” “I, za mu zo wurinka, gama kai ne Ubangiji Allahnmu.
23 In very deed the hills were liars. and the multitude of the mountains: truly in the Lord our God is the salvation of Israel.
Tabbatacce hayaniyar bin gumaka a kan tuddai da duwatsu banza ne; tabbatacce a wurin Ubangiji Allahnmu ne akwai ceton Isra’ila.
24 Confusion hath devoured the labor of our fathers from our youth, their flocks and their herds, their sons and their daughters.
Daga ƙuruciyarmu allolin kunya sun cinye mu amfanin wahalar kakanninmu garkunan tumakinsu da na awakinsu, yaransu maza da mata.
25 We shall sleep in our confusion, and our shame shall cover us, because we have sinned against the Lord our God, we and our fathers from our youth even to this day, and we have not hearkened to the voice of the Lord our God.
Bari mu kwanta mu sha kunya, bari kuma kunyarmu ta rufe mu. Mun yi wa Ubangiji Allahnmu zunubi, da mu da kakanninmu; daga ƙuruciyarmu har yă zuwa yau ba mu yi wa Ubangiji Allahnmu biyayya ba.”