< Jeremiah 13 >
1 Thus saith the Lord to me: Go, and get thee a linen girdle, and thou shalt put it about thy loins, and shalt not put it into water.
Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Tafi ka sayo abin ɗamara na lilin ka sha ɗamara da shi, amma kada ka bari yă taɓa ruwa.”
2 And I got a girdle accoding to the word of the Lord, and put it about my loins.
Saboda haka na sayo abin ɗamara, yadda Ubangiji ya umarce ni, na kuwa sha ɗamara da shi.
3 And the word of the Lord came to me the second time, saying:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini sau na biyu cewa,
4 Take the girdle which thou hast got, which is about thy loins, and arise, and go to the Euphrates, and hide it there in a hole of the rock.
“Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi yanzu zuwa Fera ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.”
5 And I went, and hid it by the Euphrates, as the Lord had commanded me.
Saboda haka na tafi na ɓoye shi a Fera, yadda Ubangiji ya ce mini.
6 And it came to pass after many days, that the Lord said to me: Arise, go to the Euphrates, and take from thence the girdle, which I commanded thee to hide there.
Bayan’yan kwanaki sai Ubangiji ya ce mini, “Tafi yanzu zuwa Fera ka ɗauko abin ɗamara da na ce maka ka ɓoye a can.”
7 And I went to the Euphrates, and digged, and took the girdle out of the place where I had hid it: and behold the girdle was rotten, so that it was fit for no use.
Sai na tafi Fera da haka na ɗauko abin ɗamara daga wurin da na ɓoye shi, amma abin ɗamara yanzu ya lalace ya zama ba shi da amfani sam.
8 And the word of the Lord came to me, saying:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
9 Thus saith the Lord: after this manner will I make the pride of Juda, and the great pride of Jerusalem to rot.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Haka zan lalatar da alfarmar Yahuda da yawan alfarmar Urushalima.
10 This wicked people, that will not hear my words, and that walk in the perverseness of their heart, and have gone after strange gods to serve them, and to adore them: and they shall be as this girdle which is fit for no use.
Waɗannan mugayen mutane, waɗanda suka ƙi saurari maganata, waɗanda suka biye wa taurin zuciyarsu suka bi waɗansu alloli don su bauta su kuma yi musu sujada, za su zama kamar wannan abin ɗamara gaba ɗaya marasa amfani!
11 For as the girdle sticketh close to the loins of a man, so have I brought close to me all of the house of Israel, and all the house of Juda, saith the Lord: that they might be my people, and for a name, and for a praise, and for a glory: but they would not hear.
Gama kamar yadda abin ɗamara kan kame gindin mutum tam, haka zan daure dukan gidan Isra’ila da dukan gidan Yahuda gare ni,’ in ji Ubangiji, ‘domin su zama jama’a, da suna, da yabo, da daraja a gare ni, amma sun ƙi ji.’
12 Thou shalt speak therefore to them this word: Thus saith the Lord God of Israel: Every bottle shall be filled with wine, and they shall say to thee: Do we not know that every bottle shall be filled with wine?
“Faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi.’ In kuwa suka ce maka, ‘Ba mu san cewa ya kamata a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi ba?’
13 And thou shalt say to them: Thus saith the Lord: Behold I will fill all the inhabitants of this land, and the kings of the race of David that sit upon his throne, and the priests, and the prophets, and all the inhabitants of Jerusalem. with drunkenness.
Sai ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan cika dukan waɗanda suke zama a ƙasar da buguwa, har ma da sarakunan da suke zama a kursiyin Dawuda, firistoci, annabawa da dukan waɗanda suke zaune a Urushalima.
14 And I will scatter them every man from his brother, and fathers and sons in like manner, saith the Lord: I will not spare, and I will not pardon: nor will I have mercy, but to destroy them.
Zan fyaɗe su a kan juna, iyaye da’ya’yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi ko jinƙai, ko juyayi ba zai hana ni hallaka su ba.’”
15 Hear ye, and give ear: Be not proud, for the Lord hath spoken.
Ku ji ku kuma saurara, kada ku yi girman kai, gama Ubangiji ya yi magana.
16 Give ye glory to the Lord your God, before it be dark, and before your feet stumble upon the dark mountains: you shall look for light, and he will turn it into the shadow of death, and into darkness.
Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnku kafin ya kawo duhu, kafin ƙafafunku su yi tuntuɓe a kan tuddai masu duhu. Za ku sa zuciya ganin haske amma zai mai da shi duhu mai kauri ya kuma canja shi zuwa duhu baƙi ƙirin.
17 But if you will not hear this, my soul shall weep in secret for your pride: weeping it shall weep, and my eyes shall run down the tears, because the flock of the Lord is carried away captive.
Amma in ba ku saurara ba, zan yi kuka a ɓoye saboda girmankanku; idanuna za su yi kuka mai zafi, suna zub da hawaye ƙwarai, domin zan kwashe garken Ubangiji zuwa zaman bauta.
18 Say to the king, and to the queen: Humble yourselves, sit down: for the crown of your glory is come down from your head.
Ka faɗa wa sarki da kuma mahaifiyar sarauniya cewa, “Ku sauko daga kursiyinku, gama rawaninku na ɗaukaka za su fāɗi daga kawunanku.”
19 The cities of the south are shut up, and there is none to open them: all Juda is carried away captive with an entire captivity.
Za a kulle biranen da suke a Negeb, kuma babu wanda zai buɗe su. Za a kwashe dukan Yahuda zuwa zaman bauta, za a kwashe su tas.
20 Lift up your eyes, and see, you that come from the north: where is the flock that is given thee, thy beautiful cattle?
Ku tā da idanunku ku ga waɗanda suke zuwa daga arewa. Ina garken da aka ba ku tumakin da kuke taƙama a kai?
21 What wilt thou say when he shall visit thee? for thou hast taught them against thee, and instructed them against thy own head: shall not sorrows lay hold on thee, as a woman in labour?
Me za ku ce sa’ad da Ubangiji ya naɗa muku waɗanda ku kanku kuka koya musu a matsayi abokai na musamman? Ashe, azaba ba za tă auko muku kamar na mace mai naƙuda ba?
22 And if thou shalt say in thy heart: Why are these things come upon me? For the greatness of thy iniquity, thy nakedness is discovered, the soles of thy feet are defiled.
In kuma kuka tambaye kanku “Me ya sa wannan ya faru da mu?” Wannan kuwa saboda yawan zunubanku ne ya sa fatarinku ya yage aka kuma wahalshe jikinku.
23 If the Ethiopian can change his skin, or the leopard his spots: you may also do well, when you have learned evil.
Mutumin Habasha zai iya canja launin fatar jikinsa ko damisa ta canja dabbare dabbarenta? Ba za ku iya yin alheri ku da kuka saba da yin mugunta ba.
24 And I will scatter them as stubble, which is carried away by the wind in the desert.
“Zan watsar da ku kamar yayin da iskar hamada take hurawa.
25 This is thy lot, and the portion of thy measure from me, saith the Lord, because thou hast forgotten me, and hast trusted in falsehood.
Rabonku ne wannan, sashen da na auka muku,” in ji Ubangiji “domin kun manta da ni kuka kuma dogara ga allolin ƙarya.
26 Wherefore I have also bared my thighs against thy face, and thy shame hath appeared.
Zan kware fatarinku sama ya rufe fuskarku don a iya ga tsiraicinku
27 I have seen thy adulteries, and thy neighing, the wickedness of thy fornication: and thy abominations, upon the hills in the field. Woe to thee, Jerusalem, wilt thou not be made clean after me: how long yet?
zinace zinacenku da haniniya kamar dawakai, karuwancinku na bankunya! Na ga ayyukanku na banƙyama a kan tuddai da kuma a filaye. Kaitonki, ya Urushalima! Har yaushe za ki ci gaba da rashin tsarki?”