< Isaiah 46 >
1 Bel is broken, Nebo is destroyed: their idols are put upon beasts and cattle, your burdens of heavy weight even unto weariness.
Bel ya rusuna, Nebo ya durƙusa ƙasa; ana ɗaukan gumakansu a kan dabbobi ne. Siffofin da ake yawo da su nawaya ne, kayan nauyi masu gajiyarwa.
2 They are consumed, and are broken together: they could not save him that carried them, and they themselves shall go into captivity.
Sun durƙusa suka kuma rusuna tare; ba su iya kuɓutar da nauyin kaya su kansu sukan tafi bauta.
3 Hearken unto me, O house of Jacob, all the remnant of the house of Israel, who are carried by my bowels, are borne up by my womb.
“Ku kasa kunne gare ni, ya ku gidan Yaƙub, dukanku waɗanda kuka rage na gidan Isra’ila, ku da na lura da ku tun da aka yi cikinku, na kuma riƙe ku tun haihuwarku.
4 Even to your old age I am the same, and to your grey hairs I will carry you: I have made you, and I will bear: I will carry and will save.
Har lokacin da kuka tsufa kuka yi furfura ni ne shi, ni ne shi wanda zai lura da ku. Na yi ku zan kuma riƙe ku; zan lura da ku in kuma kuɓutar da ku.
5 To whom have you likened me, and made me equal, and compared me, and made me like?
“Da wa za ku kwatanta ni ko ku ɗauka daidai da ni? Da wa nake kama da har da za ku kwatanta ni?
6 You that contribute gold out of the bag, and weigh out silver in the scales: and hire a goldsmith to make a god: and they fall down and worship.
Waɗansu sukan zubar da zinariya daga jaka su kuma auna azurfa a ma’auni; sukan yi haya maƙerin zinariya don yă ƙera allah, su kuma rusuna su yi masa sujada.
7 They bear him on their shoulders and carry him, and set him in his piece, and he shall stand, and shall not stir out of his place. Yea, when they shall cry also unto him, he shall not hear: he shall not save them from tribulation.
Sukan daga shi a kafaɗunsu su kuma ɗauke shi; sukan kafa shi a tsaye a wurinsa, a can kuwa zai tsaya. Daga wannan wuri ba zai iya gusawa ba. Ko da wani ya nemi taimakonsa, ba ya amsawa; ba zai iya cetonsa daga wahala ba.
8 Remember this, and be ashamed: return, ye transgressors, to the heart.
“Ku tuna da wannan, ku sa shi a zuciya, ku riƙe shi a zuciya, ku’yan tawaye.
9 Remember the former age, for I am God, and there is no God beside, neither is there the like to me:
Ku tuna da abubuwan da suka riga suka faru, waɗannan na tun dā; ni ne Allah, kuma babu wani; ni ne Allah kuma babu wani kamar ni.
10 Who shew from the beginning the things that shall be at last, and from ancient times the things that as yet are not done, saying: My counsel shall stand, and all my will shall be done:
Nakan sanar da ƙarshe tun daga farko, daga fil azal, abin da yake zuwa nan gaba. Na ce nufina zai tabbata, kuma zan aikata dukan abin da na gan dama.
11 Who call a bird from the east, and from a far country the man of my own will, and I have spoken, and will bring it to pass: I have created, and I will do it.
Daga gabas na kira tsuntsun da yake farauta; daga can ƙasa mai nesa, wani mutumin da zai cika nufina. Abin da na riga na faɗa, shi zan sa ya faru; abin da na shirya, shi zan aikata.
12 Hear me, O ye hardhearted, who are far from justice.
Ku kasa kunne, ku masu taurinkai, ku da kuke nesa da adalci.
13 I have brought my justice near, it shall not be afar off: and my salvation shall not tarry. I will give salvation in Sion, and my glory in Israel.
Ina kawo adalcina kusa, ba shi da nisa; kuma cetona ba zai jinkirta ba. Zan yi wa Sihiyona ceto, darajata ga Isra’ila.