< Isaiah 32 >
1 Behold a king shall reign in justice, and princes shell rule in judgment.
Duba, sarki zai yi mulki cikin adalci masu mulki kuma su yi mulki da adalci.
2 And a man shall be as when one is hid from the wind, and hideth himself from a storm, as rivers of waters in drought, and the shadow of a rock that standeth out in a desert land.
Kowane mutum zai zama kamar wurin fakewa daga iska mafaka kuma daga hadari, kamar rafuffukan ruwa a hamada da kuma inuwar babban dutse a ƙeƙasasshiyar ƙasa.
3 The eyes of them that see shall not be dim, and the ears of them that hear shall hearken diligently.
Sa’an nan idanun waɗanda suka gani ba za su ƙara rufewa ba, kunnuwan waɗanda suka ji kuma za su saurara.
4 And the heart of fools shall understand knowledge, and the tongue of stammerers shall speak readily and plain.
Zuciya marasa haƙuri za su sani su kuma fahimta, harshen masu ana’ana kuma zai sāke su yi magana sosai.
5 The fool shall no more be called prince: neither shall the deceitful be called great:
Ba za a ƙara ce da wawa mai girma ba ko kuwa a ɗaukaka mazambaci.
6 For the fool will speak foolish things, and his heart will work iniquity, to practise hypocrisy, and speak to the Lord deceitfully, and to make empty the soul of the hungry, and take away drink from the thirsty.
Gama wawa maganar wauta yakan yi, zuciyarsa ta cika da mugunta, yana aikata abubuwan rashin sanin Allah yana baza kurakurai game da Ubangiji; yana barin mayunwata da yunwa ya kuma hana masu ƙishirwa ruwan sha.
7 The vessels of the deceitful are most wicked: for he hath framed devices to destroy the meek, with lying words, when the poor man speaketh judgment.
Matakan mazambaci mugaye ne, yana ƙulla mugayen shirye-shirye don yă hallaka talakawa da ƙarairayi, ko sa’ad da roƙon mai bukata da gaskiya ne.
8 But the prince will devise such things as are worthy of a prince, and he shall stand above the rulers.
Amma mutumin kirki kan yi shirye-shirye masu kirki, kuma yakan tsaya a kan ayyukan kirki.
9 Rise up, ye rich women, and hear my voice: ye confident daughters, give ear to my speech.
Ku matan da kuke zaman jin daɗi, ku tashi ku saurare ni; ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya, ku ji abin da zan faɗa!
10 For after days and a year, you that are confident shall be troubled: for the vintage is at an end, the gathering shall come no more.
Cikin ɗan lokaci ƙasa da shekara guda ku da kuke tsammani kuna da kāriya za ku yi rawar jiki; girbin’ya’yan inabi zai kāsa, girbin’ya’yan itatuwa kuma ba zai zo ba.
11 Be astonished, ye rich women, be troubled, ye confident ones: strip yen, and be confounded, gird your loins.
Ku yi rawar jiki, ku mata masu jin daɗi, ku sha wahala, ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya! Ku tuɓe rigunanku, ku ɗaura tsummoki a kwankwasonku.
12 Mourn for your breasts, for the delightful country, for the fruitful vineyard.
Ku bugi ƙirjinku don gonaki masu kyau don’ya’yan inabi
13 Upon the land of my people shall thorns and briers come up: how much more upon all the houses of joy, of the city that rejoiced?
da kuma don ƙasar mutanena, da ƙasar da ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suka yi girma, I, ku yi kuka saboda dukan gidajen da dā ake biki da kuma domin wannan birnin da dā ake murna a ciki.
14 For the house is forsaken, the multitude of the city is left, darkness and obscurity are come upon its dens for ever. A joy of wild asses, the pastures of flocks,
Za a ƙyale kagarar, a gudu a bar birnin da dā ake hayaniya; mafaka da hasumiyar tsaro za su zama kango har abada, jin daɗin jakuna, makiyaya don garkuna,
15 Until the spirit be poured upon us from on high: and the desert shall be as a charmel, and charmel shall be counted for a forest.
sai an zubo Ruhu a kanmu daga sama, hamada kuma ta zama ƙasar mai taƙi, gona mai taƙi kuma ta zama kamar kurmi.
16 And judgment shall dwell in the wilderness, and justice shall sit in charmel.
Aikin gaskiya zai zauna a hamada adalci kuma zai zauna a ƙasa mai taƙi.
17 And the work of justice shall be peace, and the service of justice quietness, and security for ever.
Aikin adalci zai zama salama; tasirin adalci zai zama natsuwa da tabbaci har abada.
18 And my people shall sit in the beauty of peace, and in the tabernacles of confidence, and in wealthy rest.
Mutanena za su zauna lafiya a wuraren salama, a gidaje masu kāriya, a wuraren hutun da babu fitina.
19 But hail shall be in the descent of the forest, and the city shall be made very low.
Ko da yake ƙanƙara za tă fāɗo a jeji, a kuma rurrushe birni gaba ɗaya,
20 Blessed are ye that sow upon all waters, sending thither the foot of the ox and the ass.
zai zama muku da albarka, ku da kuke shuki iri kusa da kowane rafi, kuna kuma barin lafiyayyiyar makiyaya domin shanu da jakunanku.