< Isaiah 20 >
1 In the year that Tharthan entered into Azotus, when Sargon the king of the Assyrians had sent him, and he had fought against Azotus, and had taken it:
A shekarar da babban shugaban yaƙin da Sargon sarkin Assuriya ya aika, ya zo Ashdod ya kuma fāɗa mata ya kuma ci ta da yaƙi,
2 At that same time the Lord spoke by the hand of Isaias the son of Amos, saying: Go, and loose the sackcloth from off thy loins, and take off thy shoes from thy feet. And he did so, and went naked, and barefoot.
a wannan lokaci Ubangiji ya yi magana ta wurin Ishaya ɗan Amoz. Ya ce masa, “Tuɓe tsummokin da kake saye da su, da kuma takalman da ka sa a ƙafafu.” Ya kuwa yi haka, yana yawo tsirara kuma ba takalma a ƙafa.
3 And the Lord said: As my servant Isaias hath walked, naked and barefoot, it shall be a sign and a wonder of three years upon Egypt, and upon Ethiopia,
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kamar dai yadda bawana Ishaya ya yi ta yawo tsirara kuma ba takalmi a ƙafa shekara uku, a matsayin alama da shaida a kan Masar da Kush,
4 So shall the king of the Assyrians lead away the prisoners of Egypt, and the captivity of Ethiopia, young and old. naked and barefoot, with their buttocks uncovered to the shame of Egypt.
haka sarkin Assuriya zai kwashe kamammun Masarawa da Kushawa tsirara kuma ba takalma a ƙafa, yaro da babba, asirinsu a tsiraice, don a kunyata Masar.
5 And they shall be afraid, and ashamed of Ethiopia their hope, and of Egypt their glory.
Waɗanda suka dogara ga Kush suka yi taƙama da Masar za su ji tsoro su kuma sha kunya.
6 And the inhabitants of this isle shall say in that day: Lo this was our hope, to whom we fled for help, to deliver up from the face of the king of the Assyrians: and how shall we be able to escape?
A wannan rana mutanen da suke zama a bakin teku za su ce, ‘Dubi abin da ya faru da waɗanda muka dogara a kai, waɗanda muka gudu muka je don neman taimako da ceto daga sarkin Assuriya! Yaya za mu tsira?’”