< Isaiah 16 >

1 Send forth, O Lord, the lamb, the ruler of the earth, from Petra of the desert, to the mount of the daughter of Sion.
Ku aiko da raguna a matsayin haraji ga mai mulkin ƙasar, daga Sela a hamada, zuwa dutsen Diyar Sihiyona.
2 And it shall come to pass, that as a bird fleeing away, and as young ones flying out of the nest, so shall the daughters of Moab be in the passage of Arnon.
Kamar tsuntsaye masu firiya da aka kora daga sheƙa, haka matan Mowab suke a kogunan Arnon.
3 Take counsel, gather a council: make thy shadow as the night in the midday: hide them that flee, and betray not them that wander about.
“Ku ba mu shawara, ku yanke shawara. Ku mai da inuwarku kamar dare, a tsakar rana. Ku ɓoye masu gudun hijira, kada ku bashe masu neman mafaka.
4 My fugitives shall dwell with thee: O Moab, be thou a covert to them from the face of the destroyer: for the dust is at an end, the wretch is consumed: he hath failed, that trod the earth under foot.
Ku bar Mowabawa masu gudun hijira su zauna tare da ku; ku zama mafakarsu daga mai neman hallaka su.” Mai danniya zai zo ga ƙarshe hallaka kuma za tă daina; masu lalatar da ƙasa za su kare
5 And a throne shall be prepared in mercy, and one shall sit upon it in truth in the tabernacle of David, judging and seeking judgment and quickly rendering that which is just.
Da ƙauna za a kafa kursiyi; da aminci mutum zai zauna a kansa, wani daga gidan Dawuda, wani wanda ta shari’antawa yakan nuna gaskiya ya hanzarta yin adalci.
6 We have heard of the pride of Moab, he is exceeding proud: his pride and his arrogancy, and his indignation is more than his strength.
Mun ji fariyar Mowab, mun ji yawan fariyarta da girmankanta, fariyarta da reninta, amma taƙamarsu ta banza ce.
7 Therefore shall Moab howl to Moab, every one shall howl: to them that rejoice upon the brick walls, tell ye their stripes.
Saboda haka Mowabawa za su yi kuka mai zafi, za su yi kuka mai zafi tare saboda Mowab. Ku yi makoki ku kuma yi baƙin ciki saboda ƙosai da kuka riƙa ci a Kir Hareset.
8 For the suburbs of Hesebon are desolate, and the lords of the nations have destroyed the vineyard of Sabama: the branches thereof have reached even to Jazer: they have wandered in the wilderness, the branches thereof are left, they are gone over the sea.
Gonakin Heshbon sun bushe, inabin Sibma ma haka. Masu mulkin al’ummai sun tattake inabi mafi kyau, waɗanda suka taɓa yaɗuwa zuwa Yazer suka bazu ta wajen hamada. Tohonsu sun buɗu suka kai har teku.
9 Therefore I will lament with the weeping of Jazer the vineyard of Sabama: I will water thee with my tears, O Hesebon, and Eleale: for the voice of the treaders hath rushed in upon thy vintage, and upon thy harvest.
Saboda haka na yi kuka, yadda Yazer take kuka, saboda inabin Sibma. Ya Heshbon, ya Eleyale, na cika ku da hawaye! Sowa ta murna a kanku saboda’ya’yan itatuwanku da suka nuna da kuma girbinku sun ɓace.
10 And gladness and joy shall be taken away from Carmel, and there shall be no rejoicing nor shouting in the vineyards. He shall not tread out wine in the press that was wont to tread it out: the voice of the treaders I have taken away.
An ɗauke farin ciki da murna daga gonakin itatuwa masu’ya’ya; babu wanda yake rerawa ko yake sowa a cikin gonakin inabi; babu wanda yake matsin ruwan inabi a wuraren matsi, gama na kawo ƙarshen yin sowa.
11 Wherefore my bowels shall sound like a harp for Moab, and my inward parts for the brick wall.
Zuciyata tana makoki saboda Mowab kamar garaya, na yi baƙin ciki saboda Kir Hareset.
12 And it shall come to pass, when it is seen that Moab is wearied on his high places, that he shall go in to his sanctuaries to pray, and shall not prevail.
Sa’ad Mowab ta bayyana a masujadar bisa tudu, tana gajiyar da kanta ne kawai; sa’ad da ta tafi wurin tsafinta don tă yi addu’a, babu wani amfani.
13 This is the word, that the Lord spoke to Moab from that time:
Wannan ita ce maganar da Ubangiji ya riga ya yi game da Mowab.
14 And now the Lord hath spoken, saying: In three years, as the years of a hireling, the glory of Moab shall be taken away for all the multitude of the people, and it shall be left small and feeble, not many.
Amma yanzu Ubangiji ya ce, “Cikin shekara uku, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, haka za a mai da daraja da kuma dukan yawan mutanen Mowab abin reni, daga ɗumbun mutanenta,’yan kaɗan ne kaɗai za su ragu, za su kuma zama marasa ƙarfi.”

< Isaiah 16 >