< Hosea 1 >
1 The word of the Lord, that came to Osee the son of Beeri, in the days of Ozias, Joathan, Achaz, and Ezechias kings of Juda, and in the days of Jeroboam the son of Joas king of Israel.
Maganar Ubangiji da ta zo wa Hosiya ɗan Beyeri a zamanin mulkin Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, sarakunan Yahuda, da zamanin mulkin Yerobowam ɗan Yowash sarkin Isra’ila.
2 The beginning of the Lord’s speaking by Osse: and the Lord said to Osee: Go, take thee a wife of fornications, and have of her children of fornications: for the land by fornication shall depart from the Lord.
Sa’ad da Ubangiji ya fara magana ta wurin Hosiya, Ubangiji ya ce masa, “Ka tafi, ka auro wa kanka mazinaciya da’ya’yan da aka haifa ta hanyar rashin aminci, domin ƙasar tana da laifin mummunan zina ta wurin rabuwa da Ubangiji.”
3 So he went, and took Gomer the daughter of Debelaim: and she conceived and bore him a son.
Saboda haka sai ya auri Gomer’yar Dibilayim, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa namiji.
4 And the Lord said to him: Call his name Jezrahel: for yet a little while, and I will visit the blood of Jezrahel upon the house of Jehu, and I will cause to cease the kingdom of the house of Israel.
Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba shi suna Yezireyel, domin ba da daɗewa ba zan hukunta gidan Yehu saboda kisan da aka yi a Yezireyel, zan kuma kawo ƙarshen mulkin Isra’ila.
5 And in that day I will break in pieces the bow of Israel in the valley of Jezrahel.
A wannan rana zan karye ƙarfin Isra’ila a Kwarin Yezireyel.”
6 And she conceived again, and bore a daughter, and he said to him: Call her name, Without mercy: for I will not add any more to have mercy on the house of Israel, but I will utterly forget them.
Gomer ta sāke ɗauki ciki ta kuma haifi’ya mace. Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba ta suna, Lo-Ruhama, gama ba zan ƙara nuna wa gidan Isra’ila ƙauna ba, har da zan gafarta musu.
7 And I will have mercy on the house of Juda, and I will save them by the Lord their God: and I will not save them by bow, nor by sword, nor by battle, nor by horses, nor by horsemen.
Duk da haka zan nuna ƙauna ga gidan Yahuda; zan kuma cece su, ba da baka, takobi ko yaƙi ba, ko ta wurin dawakai, ko masu hawan dawakai ba, sai ko ta wurin Ubangiji Allahnsu.”
8 And she weaned her that was called Without mercy. And she conceived, and bore a son.
Bayan ta yaye Lo-Ruhama, sai Gomer ta sāke haifi wani ɗa namiji.
9 And he said: Call his name, Not my people: for you are not my people, and I will not be yours.
Sai Ubangiji ya ce, “Ka ba shi suna Lo-Ammi, gama ku ba mutanena ba ne, ni kuma ba Allahnku ba ne.
10 And the number of the children of Israel shall be as the sand of the sea, that is without measure, and shall not be numbered. And it shall be in the place where it shall be said to them: You are not my people: it shall be said to them: Ye are the sons of the living God.
“Duk da haka Isra’ilawa za su zama kamar yashi a bakin teku, da ba za a iya aunawa ko a ƙirga ba. A inda aka ce musu, ‘Ku ba mutanena ba ne,’ za a kira su ‘’ya’yan Allah mai rai.’
11 And the children of Juda, and the children of Israel shall be gathered together: and they shall appoint themselves one head, and shall come up out of the land: for great is the day of Jezrahel.
Mutanen Yahuda da mutanen Isra’ila za su sāke haɗu su zama ɗaya, za su kuma naɗa shugaba guda su kuma fita daga ƙasar, gama ranar za tă zama mai girma wa Yezireyel.