< Hosea 9 >
1 Rejoice not, O Israel: rejoice not as the nations do: for thou hast committed fornication against thy God, thou hast loved a reward upon every cornfloor.
Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
2 The floor and the winepress shall not feed them, and the wine shall deceive them.
Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
3 They shall not dwell in the Lord’s land: Ephraim is returned to Egypt, and hath eaten unclean things among the Assyrians.
Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
4 They shall not offer wine to the Lord, neither shall they please him: their sacrifices shall be like the bread of mourners: all that shall eat it shall be defiled: for their bread is life for their soul, it shall not enter into the house of the Lord.
Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
5 What will you do in the solemn day, in the day of the feast of the Lord?
Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
6 For behold they are gone because of destruction: Egypt shall gather them together, Memphis shall bury them: nettles shall inherit their beloved silver, the bur shall be in their tabernacles.
Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
7 The days of visitation are come, the days of repaying are come: know ye, O Israel, that the prophet was foolish, the spiritual man was mad, for the multitude of thy iniquity, and the multitude of thy madness.
Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
8 The watchman of Ephraim was with my God: the prophet is become a snare of ruin upon all his ways, madness is in the house of his God.
Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
9 They have sinned deeply, as in the days of Gabaa: he will remember their iniquity, and will visit their sin.
Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
10 I found Israel like grapes in the desert, I saw their fathers like the firstfruits of the fig tree in the top thereof: but they went in to Beelphegor, and alienated themselves to that confusion, and became abominable, as those things were, which they loved.
“Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
11 As for Ephraim, their glory hath flown away like a bird from the birth, and from the womb, and from the conception.
Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
12 And though they should bring up their children, I will make them without children among men: yea, and woe to them, when I shall depart from them.
Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
13 Ephraim, as I saw, was a Tyre founded in beauty: and Ephraim shall bring out his children to the murderer.
Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
14 Give them, O Lord. What wilt thou give them? Give them a womb without children, and dry breasts.
Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
15 All their wickedness is in Galgal, for there I hated them: for the wickedness of their devices I will cast them forth out of my house: I will love them no more, all their princes are revolters.
“Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
16 Ephraim is struck, their root is dried up, they shall yield no fruit. And if they should have issue, I will slay the best beloved fruit of their womb.
An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
17 My God will cast them away, because they hearkened not to him: and they shall be wanderers among the nations.
Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.