< Hosea 7 >
1 When I would have healed Israel, the iniquity of Ephraim was discovered, and the wickedness of Samaria, for they have committed falsehood, and the thief is come in to steal, the robber is without.
a duka sa’ad da zan warkar da Isra’ila, zunuban Efraim za su tonu za a kuma bayyana laifofin Samariya. Suna ruɗu, ɓarayi sukan fasa su shiga gidaje,’yan fashi sukan yi fashi a tituna;
2 And lest they may say in their hearts, that I remember all their wickedness: their own devices now have beset them about, they have been done before my face.
amma ba su gane cewa na tuna da dukan ayyukan muguntarsu ba. Zunubansu sun kewaye su; kullum suna a gabana.
3 They have made the king glad with their wickedness: and the princes with their lies.
“Suna faranta wa sarki zuciya da muguntarsu, shugabanni kuma da ƙarairayinsu.
4 They are all adulterers, like an oven heated by the baker: the city rested a little from the mingling of the leaven, till the whole was leavened.
Dukansu mazinata ne suna ƙuna kamar matoya wadda mai gashin burodi ba ya bukata yă tura mata wuta daga cuɗe kullu har kumburinsa.
5 The day of our king, the princes began to be mad with wine: he stretched out his hand with scorners.
A ranar bikin sarkinmu shugabanni sukan bugu da ruwan inabi, yă yi cuɗanya da masu ba’a.
6 Because they have applied their heart like an oven, when he laid snares for them: he slept all the night baking them, in the morning he himself was heated as a flaming fire.
Zukatansu suna kamar matoya; sukan kusace shi da wayo. Muguwar aniyarsu takan yi ta ci dukan dare; da safe sai ta ƙuna kamar harshen wuta.
7 They were all heated like an oven, and have devoured their judges: all their kings have fallen: there is none amongst them that calleth unto me.
Dukansu suna da zafi kamar matoya; suna kashe masu mulkinsu. Dukan sarakunansu sukan fāɗi, kuma babu waninsu da yake kira gare ni.
8 Ephraim himself is mixed among the nations: Ephraim is become as bread baked under the ashes, that is not turned.
“Efraim yana cuɗanya da al’ummai; Efraim waina ne mai fāɗi da ba a juye ba.
9 Strangers have devoured his strength, and he knew it not: yea, grey hairs also are spread about upon him, and he is ignorant of it.
Baƙi sun tsotse ƙarfinsa, amma bai gane ba. Gashi kansa ya cika da furfura, amma bai lura ba.
10 And the pride of Israel shall be humbled before his face: and they have not returned to the Lord their God, nor have they sought him in all these.
Girmankan Isra’ila ya ba da shaida a kansa, amma duk da haka bai dawo ga Ubangiji Allahnsa ko yă neme shi ba.
11 And Ephraim is become as a dove that is decoyed, not having a heart: they called upon Egypt, they went to the Assyrians.
“Efraim yana kama da kurciya, marar wayo, marar hankali, yanzu yana kira ga Masar, yanzu yana juyewa ga Assuriya.
12 And when they shall go, I will spread my net upon them: I will bring them down as the fowl of the air, I will strike them as their congregation hath heard.
Sa’ad da suka tafi, zan jefa ragata a kansu; zai janye su ƙasa kamar tsuntsayen sararin sama. Sa’ad da na ji suna tafiya tare, zan kama su.
13 Woe to them, for they have departed from me: they shall be wasted because they have transgressed against me: and I redeemed them: and they have spoken lies against me.
Kaitonsu, domin sun kauce daga gare ni! Hallaka za tă aukar musu, domin sun tayar mini! Na ƙudura in cece su amma suna faɗar ƙarya a kaina.
14 And they have not cried to me with their heart, but they howled in their beds: they have thought upon wheat and wine, they are departed from me.
Ba sa yin mini kuka da zuciyarsu amma suna ihu a kan gadajensu. Sukan taru wurin ɗaya don hatsi da ruwan inabi amma su juya mini baya.
15 And I have chastised them, and strengthened their arms: and they have imagined evil against me.
Na horar da su na kuma ƙarfafa su, amma sun ƙulla mini maƙarƙashiya.
16 They returned, that they might be without yoke: they became like a deceitful bow: their princes shall fall by the sword, for the rage of their tongue. This is their derision in the land of Egypt.
Ba sa juya ga Mafi Ɗaukaka; suna kama da tanƙwararren baka. Za a kashe shugabanninsu da takobi saboda banzan maganganunsu. Saboda wannan za a wulaƙanta su a ƙasar Masar.