< Hosea 6 >
1 In their affliction they will rise early to me: Come, and let us return to the Lord:
“Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
2 For he hath taken us, and he will heal us: he will strike, and he will cure us.
Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
3 He will revive us after two days: on the third day he will raise us up, and we shall live in his sight. We shall know, and we shall follow on, that we may know the Lord. His going forth is prepared as the morning light, and he will come to us as the early and the latter rain to the earth.
Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
4 What shall I do to thee, O Ephraim? what shall I do to thee, O Juda? your mercy is as a morning cloud, and as the dew that goeth away in the morning.
“Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
5 For this reason have I hewed them by the prophets, I have slain them by the words of my mouth: and thy judgments shall go forth as the light.
Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
6 For I desired mercy, and not sacrifice: and the knowledge of God more than holocausts.
Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
7 But they, like Adam, have transgressed the covenant, there have they dealt treacherously against me.
Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
8 Galaad is a city of workers of idols, supplanted with blood.
Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
9 And like the jaws of highway robbers, they conspire with the priests who murder in the way those that pass out Sichem: for they have wrought wickedness.
Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
10 I have seen a horrible thing in the house of Israel: the fornications of Ephraim there: Israel is defiled.
Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
11 And thou also, O Juda, set thee a harvest, when I shall bring back captivity of my people.
“Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,