< Hosea 12 >
1 Ephraim feedeth on the wind, and followeth the burning heat: all the day long he multiplied lies and desolation: and he hath made a covenant with the Assyrians, and carried oil into Egypt.
Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
2 Therefore there is a judgment of the Lord with Juda, and a visitation for Jacob: he will render to him according to his ways, and according to his devices.
Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
3 In the womb he supplanted his brother: and by his strength he had success with an angel.
A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
4 And he prevailed over the angel, and was strengthened: he wept, and made supplication to him: he found him in Bethel, and there he spoke with us.
Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
5 Even the Lord the God of hosts, the Lord is his memorial.
Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
6 Therefore turn thou to thy God: keep mercy and judgment, and hope in thy God always.
Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
7 He is like Chanaan, there is a deceitful balance in his hand, he hath loved oppression.
Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
8 And Ephraim said: But yet I am become rich, I have found me an idol: all my labours shall not find me the iniquity that I have committed.
Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
9 And I that am the Lord thy God from the land of Egypt, will yet cause thee to dwell in tabernacles, as in the days of the feast.
“Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
10 And I have spoken by the prophets, and I have multiplied visions, and I have used similitudes by the ministry of the prophets.
Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
11 If Galaad be an idol, then in vain were they in Galgal offering sacrifices with bullocks: for their altars also are as heaps in the furrows of the field.
Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
12 Jacob fled into the country of Syria, and Israel served for a wife, and was a keeper for a wife.
Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
13 But the Lord by a prophet brought Israel out of Egypt: and he was preserved by a prophet.
Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
14 Ephraim hath provoked me to wrath with his bitterness, and his blood shall come upon him, and his Lord will render his reproach unto him.
Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.