< Hosea 11 >
1 As the morning passeth, so hath the king of Israel Israel was a child, and I loved him: and I called my son out of Egypt.
“Sa’ad da Isra’ila yake yaro, na ƙaunace shi, daga Masar kuma na kira ɗana.
2 As they called them, they went away from before their face: they offered victims to Baalim, and sacrificed to idols.
Amma yawan kiran da na yi wa Isra’ila haka nesa da ni da suke ta yi. Suka miƙa hadaya ga Ba’al suka kuma ƙona turare ga siffofi.
3 And I was like a foster father to Ephraim, I carried them in my arms: and they knew not that I healed them.
Ni ne na koya wa Efraim tafiya ina kama su da hannu; amma ba su gane cewa ni ne na warkar da su ba.
4 I will draw them with the cords of Adam, with the bands of love: and I will be to them as one that taketh off the yoke on their jaws: and I put his meat to him that he might eat.
Na bishe su da linzamin alheri da tausayi, da ragamar ƙauna; Na cire karkiya daga wuyansu na kuma rusuna na ciyar da su.
5 He shall not return into the land of Egypt, but the Assyrian shall be his king: because they would not be converted.
“Ba za su koma Masar ba Assuriya kuma ba za tă yi mulki a bisansu ba saboda sun ƙi su tuba ba?
6 The sword hath begun in his cities, and it shall consume his chosen men, and shall devour their heads.
Takuba za su yi ta wulgawa a biranensu, za su hallaka sandunan ƙarafan ƙofofinsu su kuma kawo ƙarshen ƙulle-ƙullensu.
7 And my people shall long for my return: but a yoke shall be put upon them together, which shall not be taken off.
Mutanena sun ƙudura su juye daga gare ni. Ko da ma suka yi kira ga Mafi Ɗaukaka, ta ko ƙaƙa ba zai girmama su ba.
8 How shall I deal with thee, O Ephraim, shall I protect thee, O Israel? how shall I make thee as Adama, shall I set thee as Seboim? my heart is turned within me, my repentance is stirred up.
“Yaya zan ba da kai, Efraim? Yaya zan miƙa ka, Isra’ila? Yaya zan yi da kai kamar Adma? Yaya zan yi da kai kamar Zeboyim? Zuciyata ta canja a cikina; dukan tausayina ya huru.
9 I will not execute the fierceness of my wrath: I will not return to destroy Ephraim: because I am God, and not man: the holy one in the midst of thee, and I will not enter into the city.
Ba zan zartar da fushina mai zafi ba, ba kuwa zan juya in ragargaza Efraim ba. Gama ni Allah ne, ba mutum ba, Mai Tsarki a cikinku. Ba zan zo cikin fushi ba.
10 They shall walk after the Lord, he shall roar as a lion: because he shall roar, and the children of the sea shall fear.
Za su bi Ubangiji; zai yi ruri kamar zaki. Sa’ad da ya yi ruri,’ya’yansa za su zo da rawan jiki daga yamma.
11 And they shall fly away like a bird out of Egypt, and like a dove out of the land of the Assyrians: and I will place them in their own houses, saith the Lord.
Za su zo da rawan jiki kamar tsuntsaye daga Masar, kamar kurciyoyi daga Assuriya. Zan zaunar da su a cikin gidajensu,” in ji Ubangiji.
12 Ephraim hath compassed me about with denials, and the house of Israel with deceit: but Juda went down as a witness with God, and is faithful with the saints.
Mutanen Efraim sun kewaye ni da ƙarairayi, gidan Isra’ila da ruɗu. Mutanen Yahuda kuma suna yi wa Allah ƙin ji, har ma a kan Mai Tsarkin nan mai aminci.