< Hebrews 1 >

1 God, who, at sundry times and in divers manners, spoke in times past to the fathers by the prophets, last of all,
A zamanin da, Allah ya yi wa kakanin kakanninmu magana ta hanyoyi ma su yawa iri iri, ta bakin annabawa.
2 In these days hath spoken to us by his Son, whom he hath appointed heir of all things, by whom also he made the world. (aiōn g165)
Amma a zamanin nan na karshe, ya yi mana magana ta wurin Dansa, wanda ya sa magajin kome, wanda ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn g165)
3 Who being the brightness of his glory, and the figure of his substance, and upholding all things by the word of his power, making purgation of sins, sitteth on the right hand of the majesty on high.
Shi ne hasken daukakar Allah, ainihin kamanin zatinsa. Ya na rike da dukkan abubuwa ta ikon kalmarsa. Bayan da ya tsarkake zunubanmu, sai ya zauna a hannun dama na madaukaki a can sama.
4 Being made so much better than the angels, as he hath inherited a more excellent name than they.
Ta haka ya ke da fifiko a kan mala'iku, kamar yadda sunansa da ya gada yake da fifiko nesa a kan nasu.
5 For to which of the angels hath he said at any time, Thou art my Son, today have I begotten thee? And again, I will be to him a Father, and he shall be to me a Son?
Domin kuwa wanene a cikin mala'iku Allah ya taba cewa, “Kai Da na ne, yau na zama Uba a gare ka?'' kuma, “Zan kasance Uba a gareshi, shi kuma, zai kasance Da a gare ni?''
6 And again, when he bringeth in the first begotten into the world, he saith: And let all the angels of God adore him.
Kuma, da Allah ya kawo magaji a duniya, sai ya ce, “Dukan mala'ikun Allah su yi masa sujada.”
7 And to the angels indeed he saith: He that maketh his angels spirits, and his ministers a flame of fire.
A game da mala'iku kuma sai ya ce, “yakan mai da mala'ikunsa ruhohi, masu hidimarsa kuma harsunan wuta.
8 But to the Son: Thy throne, O God, is for ever and ever: a sceptre of justice is the sceptre of thy kingdom. (aiōn g165)
A game da Dan, ya ce “kursiyinka, ya Allah, na har abada abadin ne. Sandar sarautarka sanda ce ta tsantsar gaskiya. (aiōn g165)
9 Thou hast loved justice, and hated iniquity: therefore God, thy God, hath anointed thee with the oil of gladness above thy fellows.
Ka kaunaci aikin adalci, ka ki aikin sabo. Saboda haka Allah, wato Allahnka, ya shafe ka da man farin ciki fiye da tsararrakinka.”
10 And: Thou in the beginning, O Lord, didst found the earth: and the works of thy hands are the heavens.
“Tun farko, Ubangiji, kai ne ka hallici duniya. Sammai kuma aikin hannayenka ne.
11 They shall perish, but thou shalt continue: and they shall all grow old as a garment.
Za su hallaka, amma kai madawwami ne. Duk za su tsufa kamar tufafi.
12 And as a vesture shalt thou change them, and they shall be changed: but thou art the selfsame, and thy years shall not fail.
Za ka nade su kamar mayafi, za su kuma sauya, amma kai kana nan ba sakewa, Har abada shekarunka ba za su kare ba.”
13 But to which of the angels said he at any time: Sit on my right hand, until I make thy enemies thy footstool?
Amma wanene a cikin mala'ikun Allah ya taba cewa, “Zauna a hannun dama na, sai na sa makiyanka a karkashin kafafunka?''
14 Are they not all ministering spirits, sent to minister for them, who shall receive the inheritance of salvation?
Ashe, ba dukkan mala'iku bane ruhohi, wadanda Allah yakan aika, don su yi wa wadanda za su gaji ceto hidima?

< Hebrews 1 >