< Genesis 8 >
1 And God remembered Noe, and all the living creatures, and all the cattle which were with him in the ark, and brought a wind upon the earth, and the waters were abated.
Amma Allah ya tuna da Nuhu da dukan namun jeji da dabbobin da suke tare da shi a cikin jirgi, ya kuma aika da wata iska ta hura dukan duniya, ruwan kuwa ya janye.
2 The fountains also of the deep, and the flood gates of heaven were shut up, and the rain from heaven was restrained.
Aka toshe maɓuɓɓugan zurfafa da ƙofofin ambaliyar sammai, ruwan sama kuma ya daina saukowa daga sarari.
3 And the waters returned from off the earth going and coming: and they began to be abated after a hundred and fifty days.
Ruwan ya janye a hankali daga ƙasa. A ƙarshen kwanaki ɗari da hamsin ɗin, ruwan ya ragu.
4 And the ark rested in the seventh month, the seven and twentieth day of the month, upon the mountains of Armenia.
A rana ta goma sha bakwai ga watan bakwai, jirgin ya sauka a duwatsun Ararat.
5 And the waters were going and decreasing until the tenth month: for in the tenth month, the first day of the month, the tops of the mountains appeared.
Ruwan ya ci gaba da janyewa har watan goma. A rana ta fari ga watan goma kuwa ƙwanƙolin duwatsun suka bayyana.
6 And after that forty days were passed, Noe, opening the window of the ark which he had made, sent forth a raven:
Bayan kwana arba’in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi,
7 Which went forth and did not return, till the waters were dried up upon the earth.
ya saki hankaka. Hankaka ya yi ta kai da kawowa har sai da ruwa ya shanye a duniya.
8 He sent forth also a dove after him, to see if the waters had now ceased upon the face of the earth.
Sai ya saki kurciya don yă ga in ruwan ya janye daga doron ƙasa.
9 But she, not finding where her foot might rest, returned to him into the ark: for the waters were upon the whole earth: and he put forth his hand, and caught her, and brought her into the ark.
Amma kurciyar ba tă sami inda za tă sa ƙafafunta ba gama akwai ruwa a dukan doron ƙasa, saboda haka ta komo wurin Nuhu a jirgi. Ya miƙa hannunsa ya ɗauko kurciyar ya shigar da ita wurinsa a cikin jirgi.
10 And having waited yet seven other days, he again sent forth the dove out of the ark.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar daga jirgi.
11 And she came to him in the evening, carrying a bough of an olive tree, with green leaves, in her mouth. Noe therefore understood that the waters were ceased upon the earth.
Sa’ad da kurciya ta komo wurinsa da yamma, sai ga ɗanyen ganyen zaitun da ta tsinko a bakinta! Sa’an nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga duniya.
12 And he stayed yet other seven days: and he sent forth the dove, which returned not any more unto him.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar, amma a wannan ƙaro ba tă komo wurinsa ba.
13 Therefore in the six hundredth and first year, the first month, the first day of the month, the waters were lessened upon the earth, and Noe opening the covering of the ark, looked, and saw that the face of the earth was dried.
A rana ta fari ga wata na fari wanda Nuhu ya cika shekaru 601, ruwa ya shanye a ƙasa. Sai Nuhu ya buɗe murfin jirgin, ya ga cewa doron ƙasa ya bushe.
14 In the second month, the seven and twentieth day of the month, the earth was dried.
A ran ashirin da bakwai ga wata na biyu, ƙasa ta bushe ƙaƙaf.
15 And God spoke to Noe, saying:
Sa’an nan Allah ya ce wa Nuhu,
16 Go out of the ark, thou and thy wife, thy sons, and the wives of thy sons with thee.
“Fito daga jirgin, kai da matarka da’ya’yanka maza da matansu.
17 All living things that are with thee of all flesh, as well in fowls as in beasts, and all creeping things that creep upon the earth, bring out with thee, and go ye upon the earth: increase and multiply upon it.
Ka fitar da kowane iri halitta mai rai da take tare da kai waje, tsuntsaye, dabbobi, da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa, don su yi ta haihuwa, su yi yawa, su ƙaru a duniya.”
18 So Noe went out, he and his sons: his wife, and the wives of his sons with him.
Sai Nuhu ya fito tare da matarsa da’ya’yansa maza da matan’ya’yansa,
19 And all living things, and cattle, and creeping things that creep upon the earth, according to their kinds, went out of the ark.
da kowace irin dabba, da kowane mai rarrafe, da kowane irin tsuntsu, da kowane irin abu da yake tafiya a bisa duniya, suka fito daga jirgi daki-daki bisa ga irinsu.
20 And Noe built an altar unto the Lord: and taking of all cattle and fowls that were clean, offered holocausts upon the altar.
Sai Nuhu ya gina bagaden hadaya ga Ubangiji, ya ɗiba waɗansu dabbobi da tsuntsaye masu tsabta, ya yi hadaya ta ƙonawa da su a kan bagaden.
21 And the Lord smelled a sweet savour, and said: I will no more curse the earth for the sake of man: for the imagination and thought of man’s heart are prone to evil from his youth: therefore I will no more destroy every living soul as I have done.
Da Ubangiji ya ji ƙanshi mai daɗi, sai ya ce a zuciyarsa, “Ba zan ƙara la’anta ƙasa saboda mutum ba, ko da yake dukan tunanin zuciyar mutum mugu ne tun yana ƙarami. Ba kuwa zan ƙara hallaka dukan halittu masu rai, kamar yadda na yi ba.
22 All the days of the earth, seedtime and harvest, cold and heat, summer and winter, night and day, shall not cease.
“Muddin duniya tana nan, lokacin shuki da na girbi, lokacin sanyi da na zafi, lokacin damina da na rani, dare da rana ba za su daina ba.”