< Genesis 6 >
1 And after that men began to be multiplied upon the earth, and daughters were born to them,
Sa’ad da mutane suka fara ƙaruwa a duniya, aka kuma hahhaifi musu’ya’ya mata,
2 The sons of God seeing the daughters of men, that they were fair, took to themselves wives of all which they chose.
sai’ya’yan Allah maza suka ga cewa’ya’yan mutane mata suna da bansha’awa, sai suka zaɓi waɗanda suke so, suka aura.
3 And God said: My spirit shall not remain in man for ever, because he is flesh, and his days shall be a hundred and twenty years.
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ruhuna ba zai zauna a cikin mutum har abada ba, saboda shi mai mutuwa ne, kwanakinsa za su zama shekaru ɗari da arba’in ne.”
4 Now giants were upon the earth in those days. For after the sons of God went in to the daughters of men, and they brought forth children, these are the mighty men of old, men of renown.
Nefilimawa suna nan a duniya a waɗancan kwanaki, da kuma kwanakin da suka bi baya, a sa’ad da’ya’yan Allah suka kwana da’ya’yan mutane mata, suka kuma hahhaifi musu’ya’ya. Ai, su ne jarumawan dā, mutanen da suka shahara.
5 And God seeing that the wickedness of men was great on the earth, and that all the thought of their heart was bent upon evil at all times,
Ubangiji kuwa ya lura cewa muguntar mutum ta yi yawa a duniya, kuma kowane abin da yake tunani a zuciyarsa mugu ne kawai a kowanne lokaci.
6 It repented him that he had made man on the earth. And being touched inwardly with sorrow of heart,
Ubangiji ya damu da ya yi mutum a duniya, abin ya zafe shi ƙwarai.
7 He said: I will destroy man, whom I have created, from the face of the earth, from man even to beasts, from the creeping thing even to the fowls of the air, for it repenteth me that I have made them.
Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan kawar da mutum, da dabbobi, da halittu masu rarrafe a ƙasa da kuma tsuntsayen sama waɗanda na halitta, daga doron ƙasa, saboda na damu da na yi su.”
8 But Noe found grace before the Lord.
Amma Nuhu ya sami tagomashi a gaban Ubangiji.
9 These are the generations of Noe: Noe was a just and perfect man in his generations, he walked with God.
Ga tarihin Nuhu. Nuhu mutum ne mai adalci, marar abin zargi a cikin mutanen zamaninsa, ya kuma yi tafiya tare da Allah.
10 And he begot three sons, Sem, Cham, and Japheth.
Nuhu yana da’ya’ya maza uku, Shem, Ham da Yafet.
11 And the earth was corrupted before God, and was filled with iniquity.
Duniya dai ta lalace sosai a gaban Allah, ta kuma cika da tashin hankali.
12 And when God had seen that the earth was corrupted (for all flesh had corrupted its way upon the earth, )
Allah ya ga yadda duniya ta lalace, gama dukan mutane a duniya sun lalatar da rayuwarsu.
13 He said to Noe: The end of all flesh is come before me, the earth is filled with iniquity through them, and I will destroy them with the earth.
Saboda haka, Allah ya ce wa Nuhu, “Zan kawo ƙarshen dukan mutane, gama saboda su duniya ta cika da tashin hankali. Lalle zan hallaka su da kuma duniya.
14 Make thee an ark of timber planks: thou shalt make little rooms in the ark, and thou shalt pitch it within and without.
Saboda haka ka yi wa kanka jirgi da katakon Saifires, ka yi ɗakuna a cikinsa, ka shafe shi da ƙaro ciki da waje.
15 And thus shalt thou make it: The length of the ark shall be three hundred cubits: the breadth of it fifty cubits, and the height of it thirty cubits.
Ga yadda za ka gina shi; jirgin zai kasance mai tsawon ƙafa 45, fāɗinsa ƙafa 75, tsayinsa kuma ƙafa 45.
16 Thou shalt make a window in the ark, and in a cubit shalt thou finish the top of it: and the door of the ark thou shalt set in the side: with lower, middle chambers, and third stories shalt thou make it.
Ka yi masa rufi, ka kuma ba da fili inci 18 tsakanin rufin a kowane gefen jirgin. Ka sa ƙofa a gefen jirgin. Ka yi shi hawa uku, ka yi ƙofa a gefe.
17 Behold I will bring the waters of a great flood upon the earth, to destroy all flesh, wherein is the breath of life, under heaven. All things that are in the earth shall be consumed.
Ga shi zan aiko da ambaliya ruwa a duniya, in hallaka dukan mai rai da yake a ƙarƙashin sama, kowace halittar da take numfashi a cikinta. Dukan abin da yake a duniya zai hallaka.
18 And I will establish my covenant with thee, and thou shalt enter into the ark, thou and thy sons, and thy wife, and the wives of thy sons with thee.
Amma zan kafa alkawarina da kai, kai kuma za ka shiga jirgin, kai da’ya’yanka maza da matarka da matan’ya’yanka tare da kai.
19 And of every living creature of all flesh, thou shalt bring two of a sort into the ark, that they may live with thee: of the male sex, and the female.
Za ka shigar da biyu na dukan halittu masu rai, namiji da ta mace a cikin jirgin, domin su rayu tare da kai.
20 Of fowls according to their kind, and of beasts in their kind, and of every thing that creepeth on the earth according to its kind; two of every sort shall go in with thee, that they may live.
Biyu na kowane irin tsuntsu, kowace irin dabba da kuma kowace irin halitta mai rarrafe a ƙasa, za su zo wurinka domin a bar su da rai.
21 Thou shalt take unto thee of all food that may be eaten, and thou shalt lay it up with thee: and it shall be food for thee and them.
Za ka ɗauki kowane irin abinci wanda za a ci, ka adana don yă zama abincinka da nasu.”
22 And Noe did all things which God commanded him.
Nuhu ya yi kome kamar yadda Allah ya umarce shi.