< Genesis 40 >
1 After this, it came to pass, that two eunuchs, the butler and the baker of the king of Egypt, offended their lord.
Bayan ɗan lokaci, sai mai riƙon kwaf da mai tuyan sarkin Masar suka yi wa maigidansu, sarkin Masar laifi.
2 And Pharao being angry with them (now the one was chief butler, the other chief baker)
Fir’auna ya yi fushi da hafsoshin nan nasa guda biyu, shugaban masu shayarwa da shugaban masu tuya,
3 He sent them to the prison of the commander of the soldiers, in which Joseph also was prisoner,
ya kuma sa su a kurkuku a cikin gidan shugaban masu tsaro, a wannan kurkukun da aka sa Yusuf.
4 But the keeper of the prison delivered them to Joseph, and he served them. Some little time passed, and they were kept in custody.
Sai shugaban masu tsaro ya danƙa su a hannun Yusuf, ya kuwa yi musu hidima. Bayan sun jima cikin kurkuku,
5 And they both dreamed a dream the same night, according to the interpretation agreeing to themselves:
sai kowanne a cikin mutum biyun nan, mai riƙon kwaf da mai tuya na sarkin Masar, waɗanda aka sa a kurkuku, suka yi mafarki a dare ɗaya, kuma kowane mafarki ya kasance da fassara irin tasa.
6 And when Joseph was come in to them in the morning, and saw them sad,
Sa’ad da Yusuf ya zo wurinsu kashegari, sai ya ga duk sun damu.
7 He asked them, saying: Why is your countenance sadder today than usual?
Saboda haka ya tambayi hafsoshin Fir’auna, waɗanda suke a kurkuku tare da shi, a gidan maigidansa ya ce, “Me ya sa fuskokinku suke a ɓace haka?”
8 They answered: We have dreamed a dream, and there is nobody to interpret it to us. And Joseph said to them: Doth not interpretation belong to God? Tell me what you have dreamed.
Sai suka amsa, “Mu biyu, mun yi mafarki, amma babu wani da zai fassara mana su.” Sa’an nan Yusuf ya ce musu, “Fassara ba daga Allah take zuwa ba? Ku faɗa mini mafarkanku.”
9 The chief butler first told his dream: I saw before me a vine,
Sai shugaban masu shayarwa ya faɗa wa Yusuf mafarkinsa. Ya ce masa, “A cikin mafarkina, na ga kuringa a gabana,
10 On which were three branches, which by little and little sent out buds, and after the blossoms brought forth ripe grapes:
kuma a kuringar, akwai rassa uku. Nan da nan kuringar ta yi toho, ta huda, ta kuma yi nonna har suka nuna, suka zama inabi.
11 And the cup of Pharao was in my hand: and I took the grapes, and pressed them into the cup which I held, and I gave the cup to Pharao.
Kwaf Fir’auna kuwa yana a hannuna, na kuma ɗiba inabin na matse su cikin kwaf Fir’auna, na kuma sa kwaf ɗin a hannunsa.”
12 Joseph answered: This is the interpretation of the dream: The three branches are yet three days:
Yusuf ya ce masa, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Rassan nan uku, kwana uku ne.
13 After which Pharao will remember thy service, and will restore thee to thy former place: and thou shalt present him the cup according to thy office, as before thou wast wont to do.
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fitar da kai, yă maido da kai a matsayinka, za ka kuwa sa kwaf Fir’auna cikin hannunsa, kamar yadda ka saba yi sa’ad da kake mai riƙon kwaf nasa.
14 Only remember me, when it shall be well with thee, and do me this kindness: to put Pharao in mind to take me out of this prison:
Amma fa, sa’ad da kome ya zama maka da kyau, ka tuna da ni, ka kuma yi mini alheri, ka ambace ni wa Fir’auna, ka fid da ni daga wannan kurkuku.
15 For I was stolen away out of the land of the Hebrews, and here without any fault was cast into the dungeon.
Gama da ƙarfi ne aka ɗauke ni daga ƙasar Ibraniyawa, ko a nan ma ban yi wani abin da ya cancanci a sa ni cikin kurkuku ba.’”
16 The chief baker seeing that he had wisely interpreted the dream, said: I also dreamed a dream, That I had three baskets of meal upon my head:
Sa’ad da shugaban masu tuya ya ga cewa Yusuf ya ba da fassara mai gamsarwa, sai ya ce, wa Yusuf, “Ni ma na yi mafarki. A kaina, akwai kwanduna uku na burodi.
17 And that in one basket which was uppermost, I carried all meats that are made by the art of baking, and that the birds ate out of it.
A kwandon na bisa, akwai kayan iri-iri da aka toya, masu kyau domin Fir’auna, amma tsuntsaye suka ci su a kwandon da yake kaina.”
18 Joseph answered: This is the interpretation of the dream: The three baskets are yet three days:
Yusuf ya ce, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Kwanduna uku, kwanaki uku ne.
19 After which Pharao will take thy head from thee, and hang thee on a cross, and the birds shall tear thy flesh.
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fid da kai, yă rataye ka a kan itace. Tsuntsaye kuwa za su ci naman jikinka.’”
20 The third day after this was the birthday of Pharao: and he made a great feast for his servants, and at the banquet remembered the chief butler, and the chief baker.
To, a rana ta uku ne, ranar tunawa da haihuwar Fir’auna, ya kuwa yi biki wa dukan hafsoshinsa. Ya fid da shugaban masu shayarwa da kuma shugaban masu tuya a gaban hafsoshinsa.
21 And he restored the one to his place to present him the cup:
Ya mai da shugaban masu shayarwa a matsayinsa, saboda haka shugaban masu shayarwa ya sāke sa kwaf a hannun Fir’auna,
22 The other he hanged on a gibbet, that the truth of the interpreter might be shewn.
amma ya rataye shugaban masu tuya, kamar dai yadda Yusuf ya faɗa musu a fassarar mafarkan da suka yi.
23 But the chief butler, when things prospered with him, forgot his interpreter.
Shugaban masu shayarwa fa, bai tuna da Yusuf ba; ya mance da shi.