< Genesis 35 >

1 In the meantime God said to Jacob: Arise, and go up to Bethel, and dwell there, and make there an altar to God, who appeared to thee when thou didst flee from Esau thy brother.
Sa’an nan Allah ya ce wa Yaƙub, “Haura zuwa Betel ka yi zama a can, ka kuma gina bagade a can wa Allah wanda ya bayyana gare ka sa’ad da kake gudu daga ɗan’uwanka Isuwa.”
2 And Jacob having called together all his household, said: Cast away the strange gods that are among you, and be cleansed and change your garments.
Saboda haka Yaƙub ya ce wa gidansa da kuma dukan waɗanda suke tare da shi, “Ku zubar da baƙin allolin da kuke da su, ku tsarkake kanku, ku kuma canja tufafinku.
3 Arise, and let us go up to Bethel, that we may make there an altar to God: who heard me in the day of my affliction, and accompanied me in my journey.
Sa’an nan ku zo, mu haura zuwa Betel, inda zan gina bagade wa Allah wanda ya amsa mini a ranar wahalata, wanda kuma ya kasance tare da ni a dukan inda na tafi.”
4 So they gave him all the strange gods they had, and the earrings which were in their ears: and he buried them under the turpentine tree, that is behind the city of Sichem.
Saboda haka suka ba Yaƙub dukan baƙin allolin da suke da su, da zoban da suke kunnuwansu, sai Yaƙub ya binne su a ƙarƙashin itacen oak a Shekem.
5 And when they were departed, the terror of God fell upon all the cities round about, and they durst not pursue after them as they went away.
Sa’an nan suka kama hanya, tsoron Allah kuwa ya kama dukan garuruwan da suke kewayensu har babu wanda ya iya bin su.
6 And Jacob came to Luza, which is in the land of Chanaan, surnamed Bethel: he and all the people that were with him.
Yaƙub da dukan mutanen da suke tare da shi suka zo Luz (wato, Betel) a ƙasar Kan’ana.
7 And he built there an altar, and called the name of that place, The house of God: for there God appeared to him when he fled from his brother.
A can ya gina bagade, ya kuma kira wurin El Betel, gama a can ne Allah ya bayyana kansa gare shi sa’ad da yake gudu daga ɗan’uwansa.
8 At the same time Debora the nurse of Rebecca died, and was buried at the foot of Bethel under an oak: and the name of that place was called, The oak of weeping.
To, Debora, ungozomar Rebeka ta rasu aka kuma binne ta a ƙarƙashin itacen oak, ƙasa da Betel. Saboda haka aka kira wurin Allon Bakut.
9 And God appeared again to Jacob, after he returned from Mesopotamia of Syria, and he blessed him,
Bayan Yaƙub ya komo daga Faddan Aram, sai Allah ya bayyana gare shi, ya kuma albarkace shi.
10 Saying: Thou shalt not be called any more Jacob, but Israel shall be thy name. And he called him Israel.
Allah ya ce masa, “Sunanka Yaƙub ne, amma ba za a ƙara kira ka Yaƙub ba; sunanka zai zama Isra’ila.” Saboda haka ya ba shi suna Isra’ila.
11 And said to him: I am God Almighty, increase thou and be multiplied. Nations and peoples of nations shall be from thee, and kings shall come out of thy loins.
Sai Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi ta haihuwa, ka kuma riɓaɓɓanya. Al’umma da tarin al’ummai za su fito daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga jikinka.
12 And the land which I gave to Abraham and Isaac, I will give to thee, and to thy seed after thee.
Ƙasar da na ba wa Ibrahim da Ishaku, zan kuma ba ka, zan kuma ba da wannan ƙasa ga zuriyarka a bayanka.”
13 And he departed from him.
Sa’an nan Allah ya tashi sama daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi.
14 But he set up a monument of stone, in the place where God had spoken to him: pouring drink offerings upon it, and pouring oil thereon:
Yaƙub kuwa ya kafa al’amudin dutse a inda Allah ya yi magana da shi, ya zuba hadaya ta sha a kansa; ya kuma zuba mai a kansa.
15 And calling the name of that place Bethel.
Yaƙub ya kira inda Allah ya yi magana da shi, Betel.
16 And going forth from thence, he came in the springtime to the land which leadeth to Ephrata: wherein when Rachel was in travail,
Sa’an nan suka tashi daga Betel. Yayinda suna da ɗan nisa da Efrat, sai Rahila ta fara naƙuda ta kuwa sha wahala sosai.
17 By reason of her hard labour she began to be in danger, and the midwife said to her: Fear not, for thou shalt have this son also.
Sa’ad da take cikin zafin haihuwa, sai macen da ta karɓi haihuwar ta ce mata, “Kada ki ji tsoro, gama yanzu kin sami wani ɗa.”
18 And when her soul was departing for pain, and death was now at hand, she called the name of her son Benoni, that is, The son of my pain: but his father called him Benjamin, that is, The son of the right hand.
Yayinda take jan numfashinta na ƙarshe, sai ta ba wa ɗanta suna Ben-Oni. Amma mahaifinsa ya kira shi Benyamin.
19 So Rachel died, and was buried in the highway that leadeth to Ephrata, this is Bethlehem.
Ta haka Rahila ta rasu, aka kuma binne ta a hanya zuwa Efrata (wato, Betlehem).
20 And Jacob erected a pillar over her sepulchre: this is the pillar of Rachel’s monument, to this day.
Yaƙub ya kafa al’amudi bisa kabarinta, al’amudin kabarin Rahila ke nan, wanda yake can har wa yau.
21 Departing thence, he pitched his tent beyond the Flock tower.
Isra’ila ya yi gaba, ya kafa tentinsa gaba da Migdal Eder.
22 And when he dwelt in that country, Ruben went, and slept with Bala, the concubine of his father: which he was not ignorant of. Now the sons of Jacob were twelve.
Yayinda Isra’ila yana zama a wancan yanki, Ruben ya shiga ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra’ila kuwa ya ji labari. Yaƙub ya haifi’ya’ya maza goma sha biyu.
23 The sons of Lia: Ruben the first born, and Simeon, and Levi, and Juda, and Issachar, and Zabulon.
’Ya’yan Liyatu maza, Ruben shi ne ɗan fari na Yaƙub. Sauran su ne, Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar da Zebulun.
24 The sons of Rachel: Joseph and Benjamin.
’Ya’yan Rahila maza su ne, Yusuf da Benyamin.
25 The sons of Bala, Rachel’s handmaid: Dan and Nephtali.
’Ya’yan Bilha maza, mai hidimar Rahila su ne, Dan da Naftali.
26 The sons of Zelpha, Lia’s handmaid: Gad and Aser: these are the sons of Jacob, that were born to him in Mesopotamia of Syria.
’Ya’yan Zilfa maza, mai hidimar Liyatu su ne, Gad da Asher. Waɗannan su ne’ya’yan Yaƙub maza, waɗanda aka haifa masa a Faddan Aram.
27 And he came to Isaac his father in Mambre, the city of Arbee, this is Hebron: wherein Abraham and Isaac sojourned.
Yaƙub ya dawo gida wurin mahaifinsa Ishaku a Mamre, kusa da Kiriyat Arba (wato, Hebron), inda Ibrahim da Ishaku suka zauna.
28 And the days of Isaac were a hundred and eighty years.
Ishaku ya rayu shekaru ɗari da tamanin,
29 And being spent with age he died, and was gathered to his people, being old and full of days: and his sons Esau and Jacob buried him.
sa’an nan ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuwa mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa da kyakkyawan tsufa da kuma cikakken shekaru.’Ya’yansa maza, Isuwa da Yaƙub suka binne shi.

< Genesis 35 >