< Genesis 10 >
1 These are the generations of the sons of Noe: Sem, Cham, and Japheth: and unto them sons were born after the flood.
Wannan shi ne labarin Shem, Ham da Yafet,’ya’yan Nuhu maza, waɗanda su ma sun haifi’ya’ya maza bayan ambaliyar.
2 The sons of Japheth: Gomer, and Magog, and Madai, and Javan, and Thubal, and Mosoch, and Thiras.
’Ya’yan Yafet maza su ne, Gomer, Magog, Madai da Yaban, Tubal, Meshek, da kuma Tiras.
3 And the sons of Gomer: Ascenez and Riphath and Thogorma.
’Ya’yan Gomer maza su ne, Ashkenaz, Rifat, da Togarma.
4 And the sons of Javan: Elisa and Tharsis, Cetthim and Dodanim.
’Ya’yan maza Yaban su ne, Elisha, Tarshish, Kittim da Rodanim.
5 By these were divided the islands of the Gentiles in their lands, every one according to his tongue and their families in their nations.
(Daga waɗannan mutane ne masu zama a bakin teku suka bazu zuwa cikin ƙasashensu da kuma cikin al’ummansu, kowanne da yarensa.)
6 And the sons of Cham: Chus, and Mesram, and Phuth, and Chanaan.
’Ya’yan Ham maza su ne, Kush, Masar, Fut, da Kan’ana.
7 And the sons of Chus: Saba, and Hevila, and Sabatha, and Regma, and Sabatacha. The sons of Regma: Saba and Dadan.
’Ya’yan Kush maza su ne, Seba, Hawila, Sabta, Ra’ama da Sabteka.’Ya’yan Ra’ama maza kuwa su ne, Sheba da Dedan.
8 Now Chus begot Nemrod: he began to be mighty on the earth.
Kush shi ne mahaifin Nimrod wanda ya yi girma ya zama jarumin yaƙi a duniya.
9 And he was a stout hunter before the Lord. Hence came a proverb: Even as Nemrod the stout hunter before the Lord.
Shi babban maharbi ne a gaban Ubangiji. Shi ya sa akan ce, kamar Nimrod babban maharbi a gaban Ubangiji.
10 And the beginning of his kingdom was Babylon, and Arach, and Achad, and Chalanne in the land of Sennaar.
Cibiyoyin mulkinsa na farko su ne Babilon, Erek, Akkad, da Kalne a cikin Shinar.
11 Out of that land came forth Assur, and built Ninive, and the streets of the city, and Chale.
Daga wannan ƙasa, sai ya tafi Assuriya, inda ya gina Ninebe, Rehobot Ir, Kala
12 Resen also between Ninive and Chale: this is the great city.
da Resen, wadda take tsakanin Ninebe da Kala; wanda yake babban birni.
13 And Mesraim begot Ludim, and Anamim, and Laabim, Nepthuim,
Mizrayim shi ne mahaifin Ludiyawa, Anamawa, Lehabiyawa, Naftuhiyawa,
14 And Phetrusim, and Chasluim; of whom came forth the Philistines, and the Capthorim.
Fetrusiyawa, da Kasluhiyawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa.
15 And Chanaan begot Sidon, his firstborn, the Hethite,
Kan’ana shi ne mahaifin, Sidon ɗan farinsa, da na Hittiyawa,
16 And the Jebusite, and the Amorrhite, and the Gergesite,
Yebusiyawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,
17 The Hevite and the Aracite: the Sinite,
Hiwiyawa, Arkiyawa, Siniyawa,
18 And the Aradian, the Samarite, and the Hamathite: and afterwards the families of the Chanaanites were spread abroad.
Arbadiyawa, Zemarawa, da Hamawa. Daga baya zuriyar Kan’aniyawa suka yaɗu
19 And the limits of Chanaan were from Sidon as one comes to Gerara even to Gaza, until thou enter Sodom and Gomorrha, and Adama, and Seboim even to Lesa.
har iyakar Kan’ana ta kai Sidon ta wajen Gerar har zuwa Gaza, sa’an nan ta milla zuwa Sodom, Gomorra, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.
20 These are the children of Cham in their kindreds, and tongues, and generations, and lands, and nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Ham maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
21 Of Sem also, the father of all the children of Heber, the elder brother of Japheth, sons were born.
Aka kuma haifa wa Shem, wan Yafet,’ya’ya maza. Shem shi ne kakan’ya’yan Eber duka.
22 The sons of Sem: Elam and Assur, and Arphaxad, and Lud, and Aram.
’Ya’yan Shem maza su ne, Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da Aram.
23 The sons of Aram: Us and Hull, and Gether, and Mess.
’Ya’yan Aram maza su ne, Uz, Hul, Geter da Mash.
24 But Arphaxad begot Sale, of whom was born Heber.
Arfakshad ne mahaifin Shela. Shela kuma shi ne mahaifin Eber.
25 And to Heber were born two sons: the name of the one was Phaleg, because in his days the earth was divided: and his brother’s name Jectan.
Aka haifa wa Eber’ya’ya maza biyu. Aka ba wa ɗaya suna Feleg, gama a zamaninsa ne aka raba duniya; aka kuma sa wa ɗan’uwansa suna Yoktan.
26 Which Jectan begot Elmodad, and Saleph, and Asarmoth, Jare,
Yoktan shi ne mahaifin, Almodad, Shelef, Hazarmawet, Yera,
27 And Aduram, and Uzal, and Decla,
Hadoram, Uzal, Dikla,
28 And Ebal, and Abimael, Saba,
Obal, Abimayel, Sheba,
29 And Ophir, and Hevila, and Jobab. All these were the sons of Jectan.
Ofir, Hawila da Yobab. Dukan waɗannan’ya’yan Yoktan maza ne.
30 And their dwelling was from Messa as we go on as far as Sephar, a mountain in the east.
Yankin da suka zauna ya miƙe daga Mesha zuwa wajen Sefar a gabashin ƙasar tudu.
31 These are the children of Sem according to their kindreds and tongues, and countries in their nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Shem maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
32 These are the families of Noe, according to their peoples and nations. By these were the nations divided on the earth after the flood.
Waɗannan su ne zuriyar’ya’yan Nuhu maza bisa ga jerin zuriyarsu cikin al’ummominsu. Daga waɗannan ne al’ummomi suka bazu ko’ina a duniya bayan ambaliya.