< Ezekiel 23 >
1 And the word of the Lord came to me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Son of man, there were two women, daughters of one mother.
“Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
3 And they committed fornication in Egypt, in their youth they committed fornication: there were their breasts pressed down, and the teats of their virginity were bruised.
Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
4 And their names were Oolla the elder, and Ooliba her younger sister: and I took them, and they bore sons and daughters. Now for their names, Samaria is Oolla, and Jerusalem is Ooliba.
Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
5 And Oolla committed fornication against me, and doted on her lovers, on the Assyrians that came to her,
“Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
6 Who were clothed with blue, princes, and rulers, beautiful youths, all horsemen, mounted upon horses.
waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
7 And she committed her fornications with those chosen men, all sons of the Assyrians: and she defiled herself with the uncleanness of all them on whom she doted.
Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
8 Moreover also she did not forsake her fornications which she had committed in Egypt: for they also lay with her in her youth, and they bruised the breasts of her virginity, and poured out their fornication upon her.
Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
9 Therefore have I delivered her into the hands of her lovers, into the hands of the sons of the Assyrians, upon whose lust she doted.
“Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
10 They discovered her disgrace, took away her sons and daughters, and slew her with the sword: and they became infamous women, and they executed judgments in her.
Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
11 And when her sister Ooliba saw this, she was mad with lust more than she: and she carried her fornication beyond the fornication of her sister.
“Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
12 Impudently prostituting herself to the children of the Assyrians, the princes, and rulers that came to her, clothed with divers colours, to the horsemen that rode upon horses, and to young men all of great beauty.
Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
13 And I saw that she was defiled, and that they both took one way.
Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
14 And she increased her fornications: and when she had seen men painted on the wall, the images of the Chaldeans set forth in colours,
“Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
15 And girded with girdles about their reins, and with dyed turbans on their heads, the resemblance of all the captains, the likeness of the sons of Babylon, and of the land of the Chaldeans wherein they were born,
da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
16 She doted upon them with the lust of her eyes, and she sent messengers to them into Chaldea.
Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
17 And when the sons of Babylon were come to her to the bed of love, they defiled her with their fornications, and she was polluted by them, and her soul was glutted with them.
Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
18 And she discovered her fornications, and discovered her disgrace: and my soul was alienated from her, as my soul was alienated from her sister.
Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
19 For she multiplied her fornications, remembering the days of her youth, in which she played the harlot in the land of Egypt.
Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
20 And she was mad with lust after lying with them whose flesh is as the flesh of asses: and whose issue as the issue of horses.
A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
21 And thou hast renewed the wickedness of thy youth, when thy breasts were pressed in Egypt, and the papa of thy virginity broken.
Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
22 Therefore, Ooliba, thus saith the Lord God: Behold I will raise up against thee all thy lovers with whom thy soul hath been glutted: and I will gather them together against thee round about.
“Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
23 The children of Babylon, and all the Chaldeans, the nobles, and the kings, and princes, all the sons of the Assyrians, beautiful young men, all the captains, and rulers, the princes of princes, and the renowned horsemen.
Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
24 And they shall come upon thee well appointed with chariot and wheel, a multitude of people: they shall be armed against thee on every side with breastplate, and buckler, and helmet: and I will set judgment before them, and they shall judge thee by their judgments.
Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
25 And I will set my jealousy against thee, which they shall execute upon thee with fury: they shall cut off thy nose and thy ears: and what remains shall fall by the sword: they shall take thy sons, and thy daughters, and thy residue shall be devoured by fire.
Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
26 And they shall strip thee of thy garments, and take away the instruments of thy glory.
Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
27 And I will put an end to thy wickedness in thee, and thy fornication brought out of the land of Egypt: neither shalt thou lift up thy eyes to them, nor remember Egypt any more.
Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
28 For thus saith the Lord God: Behold, I will deliver thee into the hands of them whom thou hatest, into their hands with whom thy soul hath been glutted.
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
29 And they shall deal with thee in hatred, and they shall take away all thy labours, and shall let thee go naked, and full of disgrace, and the disgrace of thy fornication shall be discovered, thy wickedness, and thy fornications.
Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
30 They have done these things to thee, because thou hast played the harlot with the nations among which thou wast defiled with their idols.
sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
31 Thou hast walked in the way of thy sister, and I will give her cup into thy hand.
Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
32 Thus saith the Lord God: Thou shalt drink thy sister’s cup, deep, and wide: thou shalt be had in derision and scorn, which containeth very much.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
33 Thou shalt be filled with drunkenness, and sorrow: with the cup of grief, and sadness, with the cup of thy sister Samaria.
Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
34 And thou shalt drink it, and shalt drink it up even to the dregs, and thou shalt devour the fragments thereof, thou shalt rend thy breasts: because I have spoken it, saith the Lord God.
Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
35 Therefore thus saith the Lord God: Because thou hast forgotten me, and hast cast me off behind thy back, bear thou also thy wickedness, and thy fornications.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
36 And the Lord spoke to me, saying: Son of man, dost thou judge Oolla, and Ooliba, and dost thou declare to them their wicked deeds?
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
37 Because they have committed adultery, and blood is in their hands, and they have committed fornication with their idols: moreover also their children, whom they bore to me, they have offered to them to be devoured.
gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
38 Yea, and they have done this to me. They polluted my sanctuary on the same day, and profaned my sabbaths.
Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
39 And when they sacrificed their children to their idols, and went into my sanctuary the same day to profane it: they did these things even in the midst of my house.
A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
40 They sent for men coming from afar, to whom they had sent a messenger: and behold they came: for whom thou didst wash thyself, and didst paint thy eyes, and wast adorned with women’s ornaments.
“Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
41 Thou sattest on a very fine bed, and a table was decked before thee: whereupon thou didst set my incense, and my ointment.
Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
42 And there was in her the voice of a multitude rejoicing: and to some that were brought of the multitude of men, and that came from the desert, they put bracelets on their hands, and beautiful crowns on their heads.
“Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
43 And I said to her that was worn out in her adulteries: Now will this woman still continue in her fornication.
Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
44 And they went in to her, as to a harlot: so went they in unto Oolla, and Ooliba, wicked women.
Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
45 They therefore are just men: these shall judge them as adulteresses are judged, and as shedders of blood are judged: because they are adulteresses, and blood is in their hands.
Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
46 For thus saith the Lord God: Bring a multitude upon them, and deliver them over to tumult and rapine:
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
47 And lee the people stone them with stones, and let them be stabbed with their swords: they shall kill their sons and daughters, and their houses they shall burn with fire.
Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
48 And I will take away wickedness out of the land: and all women shall learn, not to do according to the wickedness of them.
“Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
49 And they shall render your wickedness upon you, and you shall bear the sins of your idols: and you shall know that I am the Lord God.
Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”