< Ezekiel 13 >
1 And the word of the Lord came to me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Son of man, prophesy thou against the prophets of Israel that prophesy: and thou shalt say to them that prophesy out of their own heart: Hear ye the word of the Lord:
“Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
3 Thus saith the Lord God: Woe to the foolish prophets that follow their own spirit, and see nothing.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
4 Thy prophets, O Israel, were like foxes in the deserts.
Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
5 You have not gone up to face the enemy, nor have you set up a wall for the house of Israel, to stand in battle in the day of the Lord.
Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
6 They see vain things, and they foretell lies, saying: The Lord saith: whereas the Lord hath not sent them: and they have persisted to confirm what they have said.
Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
7 Have you not seen a vain vision and spoken a lying divination: and you say: The Lord saith: whereas I have not spoken.
Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
8 Therefore thus saith the Lord God: Because you have spoken vain things, and have seen lies: therefore behold I come against you, saith the Lord God.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 And my hand shall be upon the prophets that see vain things, and that divine lies: they shall not be in the council of my people, nor shall they be written in the writing of the house of Israel, neither shall they enter into the land of Israel, and you shall know that I am the Lord God.
Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
10 Because they have deceived my people, saying: Peace, and there is no peace: and the people built up a wall, and they daubed it with dirt without straw.
“‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
11 Say to them that daub without tempering, that it shall fall: for there shall be an overflowing shower, and I will cause great hailstones to fall violently from above, and a stormy wind to throw it down.
saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
12 Behold, when the wall is fallen: shall it not be said to you: Where is the daubing wherewith you have daubed it?
Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
13 Therefore thus saith the Lord God: Lo, I will cause a stormy wind to break forth in my indignation, and there shall be an overflowing shower in my anger: and great hailstones in my wrath to consume.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
14 And I will break down the wall that you have daubed with untempered mortar: and I will make it even with the ground, and the foundation thereof shall be laid bare: and it shall fall, and shall be consumed in the midst thereof: and you shall know that I am the Lord.
Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
15 And I will accomplish my wrath upon the wall, and upon them that daub it without tempering the mortar, and I will say to you: The wall is no more, and they that daub it are no more.
Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
16 Even the prophets of Israel that prophesy to Jerusalem, and that see visions of peace for her: and there is no peace, saith the Lord God.
waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
17 And thou, son of man, set thy face against the daughters of thy people that prophesy out of their own heart: and do thou prophesy against them,
“To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
18 And say: Thus saith the Lord God: Woe to them that sew cushions under every elbow: and make pillows for the heads of persons of every age to catch souls: and when they caught the souls of my people, they gave life to their souls.
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
19 And they violated me among my people, for a handful of barley, and a piece of bread, to kill souls which should not die, and to save souls alive which should not live, telling lies to my people that believe lies.
Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
20 Therefore thus saith the Lord God: Behold I declare against your cushions, wherewith you catch flying souls: and I will tear them off from your arms: and I will let go the souls that you catch, the souls that should fly.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
21 And I will tear your pillows, and will deliver my people out of your hand, neither shall they be any more in your hands to be a prey: and you shall know that I am the Lord.
Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
22 Because with lies you have made the heart of the just to mourn, whom I have not made sorrowful: and have strengthened the hands of the wicked, that he should not return from his evil way, and live.
Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
23 Therefore you shall not see vain things, nor divine divinations any more, and I will deliver my people out of your hand: and you shall know that I am the Lord.
saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”