< Ezekiel 10 >

1 And saw and behold in the firmament that was over the heads of the cherubims, there appeared over them as it were the sapphire stone, as the appearance of the likeness of a throne.
Na duba, sai na ga kamannin kursiyin saffaya a kan sararin da yake a bisa kawunan kerubobi.
2 And he spoke to the man, that was clothed with linen, and said: Go in between the wheels that are under the cherubims and fill thy hand with the coals of fire that are between the cherubims, and pour them out upon the city. And he went in, in my sight:
Sai Ubangiji ya ce wa mutumin da yake saye da lilin, “Ka shiga cikin da’irorin da suke ƙarƙashin kerubobi. Ka cika hannuwanka da garwashin wuta wanda yake tsakanin kerubobin ka kuma watsar da su a kan birnin.” Yayinda nake dubawa, sai ya shiga.
3 And the cherubims stood on the right side of the house, when the man went in, and a cloud filled the inner court.
Kerubobin kuwa suna tsaye a gefen kudu na haikali sa’ad da mutumin ya shiga, sai girgije ya cika filin da yake can ciki.
4 And the glory of the Lord was lifted up from above the cherub to the threshold of the house: and the house was filled with the cloud, and the court was filled with the brightness of the glory of the Lord.
Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa kerubobi ya tafi zuwa madogarar ƙofar haikali. Girgijen ya cika haikali, filin kuwa ya cika da hasken ɗaukakar Ubangiji.
5 And the sound of the wings of the cherubims was heard even to the outward court as the voice of God Almighty speaking.
Sai aka ji ƙarar fikafikan kerubobin har a filin waje, kamar muryar Allah Maɗaukaki sa’ad da ya yi magana.
6 And when he had commanded the man that was clothed with linen, saying: Take fire from the midst of the wheels that are between the cherubims: he went in and stood beside the wheel,
Sa’ad da Ubangiji ya umarci mutumin da yake saye da lilin cewa, “Ka ɗibi wuta daga cikin tsakanin da’irorin, daga tsakanin kerubobin,” sai mutumin ya shiga ya tsaya kusa da da’irar.
7 And one cherub stretched out his arm from the midst of the cherubims to the fire that was between the cherubims: and he took, and put it into the hands of him that was clothed with linen: who took it and went forth.
Sa’an nan ɗaya daga cikin kerubobin ya miƙa hannu zuwa wurin wutar da take tsakaninsu. Ya ɗebo wutar daga ciki ya zuba a hannuwan mutumin da yake saye da lilin, shi kuwa ya karɓa ya fita.
8 And there appeared in the cherubims the likeness of a man’s hand under their wings.
(A ƙarƙashin fikafikan kerubobin ana iya ganin abin da ya yi kamar hannuwan mutum.)
9 And I saw, and behold there were four wheels by the cherubims: one wheel by one cherub, and another wheel by another cherub: and the appearance of the wheels was to the sight like the chrysolite stone:
Na duba, sai na ga kusa da kerubobin akwai da’irori huɗu, kowanne kusa da kerub guda; da’irorin suna ƙyalli kamar wani dutse mai daraja.
10 And as to their appearance, all four were alike: as if a wheel were in the midst of a wheel.
Game da kamanninsu kuwa, huɗu a cikinsu sun yi kama da juna; kowanne ya yi kamar da da’ira a cikin da’ira.
11 And when they went, they went by four ways: and they turned not when they went: but to the place whither they first turned, the rest also followed, and did not turn back.
Yayinda suke tafiya, sukan tafi kowane gefe huɗun da kerubobin suka nufa; da’irorin ba sa juyawa yayinda kerubobin suke tafiya. Kerubobin suka tafi kowane gefen da kan ya nufa, ba tare da juyawa ba sa’ad da suke tafiya.
12 And their whole body, and their necks, and their hands, and their wings, and the circles were full of eyes, round about the four wheels.
Jikunansu gaba ɗaya, har da bayansu, hannuwansu da fikafikansu, sun cika gaba ɗaya da idanu, kamar yadda suke a da’irori huɗun.
13 And these wheels he called voluble, in my hearing.
Na ji ana kiran da’irorin “da’irorin guguwa.”
14 And every one had four faces: one face was the face of a cherub, and the second face, the face of a man: and in the third was the face of a lion: and in the fourth the face of an eagle.
Kowane daga kerubobin yana da fuskoki huɗu. Fuska ɗaya na kerub ne, na biyun fuskar mutum ne, na ukun fuskar zaki ne, na huɗun kuwa fuskar gaggafa ce.
15 And the cherubims were lifted up: this is the living creature that I had seen by the river Chobar.
Sai kerubobin suka tashi sama. Waɗannan ne halittu masu ran da na gani kusa da Kogin Kebar.
16 And when the cherubims went, the wheels also went by them: and when the cherubims lifted up their wings, to mount up from the earth, the wheels stayed not behind, but were by them.
Sa’ad da kerubobin suka motsa, sai da’irorin da suke kusa da su su motsa; kuma sa’ad da kerubobin suka buɗe fikafikansu don su tashi daga ƙasa, da’irorin ba sa barin wurarensu.
17 When they stood, these stood: and when they were lifted up, these were lifted up: for the spirit of life was in them.
Sa’ad da kerubobin suka tsaya cik, su ma sukan tsaya cik; kuma sa’ad da kerubobin suka tashi, sai su ma su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun yana a cikinsu.
18 And the glory of the Lord went forth from the threshold of the temple: and stood over the cherubims.
Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa madogarar ƙofar haikali ya kuma tsaya a bisa kerubobi.
19 And the cherubims lifting up their wings, were raised from the earth before me: and as they went out, the wheels also followed: and it stood in the entry of the east gate of the house of the Lord: and the glory of the God of Israel was over them.
Yayinda nake duba, kerubobin suka buɗe fikafikansu suka kuma tashi daga ƙasa, yayinda suka tafi kuwa, da’irorin suka tafi tare da su. Suka tsaya a mashigin ƙofar gabas na gidan Ubangiji, ɗaukakar Allah na Isra’ila kuwa yana a kansu.
20 This is the living creature, which I saw under the God of Israel by the river Chobar: and I understood that they were cherubims.
Waɗannan ne rayayyun halittun da na gani a ƙarƙashin Allah na Isra’ila kusa da Kogin Kebar, na kuma gane cewa su kerubobi ne.
21 Each one had four faces, and each one had four wings: and the likeness of a man’s hand was under their wings.
Kowanne yana da fuskoki huɗu da fikafikai huɗu, a ƙarƙashin kuwa akwai wani abin da ya yi kamar hannuwan mutum.
22 And as to the likeness of their faces, they were the same faces which I had seen by the river Chobar, and their looks, and the impulse of every one to go straight forward.
Fuskokinsu suna da kamanni ɗaya da waɗanda na gani kusa da Kogin Kebar. Kowanne ya tafi kai tsaye sosai.

< Ezekiel 10 >