< Exodus 40 >

1 And the Lord spoke to Moses, saying:
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
2 The first month, the first day of the month, thou shalt set up the tabernacle of the testimony,
“Ka kafa tabanakul, da Tentin Sujada, a kan rana ta fari ga watan fari.
3 And shalt put the ark in it, and shalt let down the veil before it:
Ka sa akwatin Alkawari a cikinsa, sa’an nan ka rufe shi da labule.
4 And thou shalt bring in the table, and set upon it the things that are commanded according to the rite. The candlestick shall stand with its lamps,
Ka shigar da teburin ka shirya kayayyakin a kansa. Sa’an nan ka shigar da wurin ajiye fitilan ka kuma sa fitilunsa.
5 And the altar of gold whereon the incense is burnt, before the ark of the testimony. Thou shalt put the hanging in the entry of the tabernacle,
Ka sa bagaden zinariya na ƙona turare a gaban akwatin Alkawari, ka kuma sa labule a ƙofar shiga tabanakul.
6 And before it the altar of holocaust:
“Ka ajiye bagade na yin hadaya ta ƙonawa a gaban ƙofar tabanakul, da Tentin Sujada;
7 The laver between the altar and the tabernacle, and thou shalt fill it with water.
ka ajiye daron tsakanin Tentin Sujada da bagaden, ka kuma zuba ruwa a cikinsa.
8 And thou shalt encompass the court with hangings, and the entry thereof.
Ka yi fili kewaye da shi, ka kuma sa labule a ƙofar shiga filin.
9 And thou shalt take the oil of unction and anoint the tabernacle with its vessels, that they may be sanctified:
“Ka ɗauki man shafewa ka shafe tabanakul da duka abin da yake cikinsa; ka keɓe shi da dukan kayayyakinsa, zai zama tsarkake.
10 The altar of holocaust and all its vessels:
Sa’an nan ka shafe bagaden hadaya ta ƙonawa da kayansa; ka keɓe bagaden, zai zama mai tsarki.
11 The laver with its foot: thou shalt consecrate all with the oil of unction, that they may be most holy.
Ka shafe daron da wurin ajiyarsa, ka kuma keɓe su.
12 And thou shalt bring Aaron and his sons to the door of the tabernacle of the testimony, and having washed them with water,
“Ka kawo Haruna da’ya’yansa a ƙofar Tentin Sujada ka wanke su da ruwa.
Sa’an nan ka sa wa Haruna tsarkakun riguna, ka shafe shi, ka kuma keɓe shi don yă yi mini hidima a matsayin firist.
Ka kawo’ya’yansa maza ka sa musu taguwoyi.
15 Thou shalt put on them the holy vestments, that they may minister to me, and that the unction of them may prosper to an everlasting priesthood.
Ka shafe su yadda ka shafe mahaifinsu, don su yi mini hidima a matsayin firistoci. Shafe musu man, zai sa su zama firistoci na ɗinɗinɗin, dukan zamanansu.”
16 And Moses did all that the Lord had commanded.
Musa ya aikata dukan kome yadda Ubangiji ya umarce shi.
17 So in the first month of the second year, the first day of the month, the tabernacle was set up.
Da haka aka kafa tabanakul, a rana ta fari ga wata na fari a shekara ta biyu.
18 And Moses reared it up, and placed the boards and the sockets and the bars, and set up the pillars,
Sa’ad da Musa ya kafa tabanakul, ya sa rammuka a wurinsu, ya sa katakan, ya kuma sa sandunan, ya kakkafa dogayen sandunan.
19 And spread the roof over the tabernacle, putting over it a cover, as the Lord had commanded.
Sa’an nan ya shimfiɗa tentin a bisa tabanakul, ya kuma sa murfi a bisa tentin, yadda Ubangiji ya umarce shi.
20 And he put the testimony in the ark, thrusting bars underneath, and the oracle above.
Ya ɗauki dokokin Alkawari ya sa a cikin akwatin, ya kuma zura sandunan a zoban akwatin, sa’an nan ya sa murfin kafara a bisansa.
21 And when he had brought the ark into the tabernacle, he drew the veil before it to fulfill the commandment of the Lord.
Sai ya kawo akwatin a cikin tabanakul, ya kuma rataye labulen rufewa ya tsare akwatin Alkawarin, yadda Ubangiji ya umarce shi.
22 And he set the table in the tabernacle of the testimony at the north side without the veil,
Musa ya sa teburin a Tentin Sujada, a gefen arewa na tabanakul waje da labulen.
23 Setting there in order the loaves of proposition, as the Lord had commanded Moses.
Ya shirya burodin a kai a gaban Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
24 He set the candlestick also in the tabernacle of the testimony over against the table on the south side,
Ya sa wurin ajiye fitilan a Tentin Sujada ɗaura da teburin a gefen kudu na tabanakul
25 Placing the lamps in order, according to the precept of the Lord.
ya kuma shirya fitilun a gaban Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
26 He set also the altar of gold under the roof of the testimony over against the veil,
Musa ya sa bagaden zinariya a cikin Tentin Sujada a gaban labulen
27 And burnt upon it the incense of spices, as the Lord had commanded Moses.
ya ƙone turare mai ƙanshi a kai, yadda Ubangiji ya umarce shi.
28 And he put also the hanging in the entry of the tabernacle of the testimony,
Sa’an nan ya sa labule a ƙofar shiga na tabanakul.
29 And the altar of holocaust of the entry of the testimony, offering the holocaust, and the sacrifices upon it, as the Lord had commanded.
Ya sa bagaden hadaya ta ƙonawa kusa da ƙofar tabanakul, Tentin Sujada, sa’an nan ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta gari a kansa, yadda Ubangiji ya umarce shi.
30 And he set the laver between the tabernacle of the testimony and the altar, filling it with water.
Ya sa daro tsakanin Tentin Sujada da bagade, ya kuma zuba ruwa a cikinsa don wanki,
31 And Moses and Aaron, and his sons washed their hands and feet,
a cikin kuwa Musa da Haruna da’ya’yansa maza sukan wanke hannunsa da ƙafafunsu.
32 When they went into the tabernacle of the covenant, and went to the altar, as the Lord had commanded Moses.
Sukan yi wanka a duk sa’ad da suka shiga Tentin Sujada, ko in suka kusaci bagade, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
33 He set up also the court round about the tabernacle and the altar, drawing the hanging in the entry thereof. After all things were perfected,
Sa’an nan Musa ya yi fili kewaye da tabanakul da kuma bagaden, ya rataye labule a ƙofar shiga filin. Da haka Musa ya gama aikin.
34 The cloud covered the tabernacle of the testimony, and the glory of the Lord filled it.
Sa’an nan girgije ya rufe Tentin Sujada sai ɗaukakar Ubangiji ta cika tabanakul.
35 Neither could Moses go into the tabernacle of the covenant, the cloud covering all things and the majesty of the Lord shining, for the cloud had covered all.
Musa bai iya shiga Tentin Sujada ba domin girgije ya riga ya sauka a kansa, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika tabanakul.
36 If at any time the cloud removed from the tabernacle, the children of Israel went forward by their troops:
Cikin tafiyar Isra’ilawa duka, sukan kama tafiyarsu ne a duk sa’ad da girgijen ya tashi daga kan tabanakul.
37 If it hung over, they remained in the same place.
Idan girgijen bai tashi ba, ba za su tashi ba, sai a ranar da ya tashi.
38 For the cloud of the Lord hung over the tabernacle by day, and a fire by night, in the sight of all the children of Israel throughout all their mansions.
Gama a cikin tafiyarsu duka, girgijen Ubangiji yana kan tabanakul da rana, da dare kuwa wuta yake cikinsa domin dukan Isra’ilawa su gani.

< Exodus 40 >