< Exodus 16 >

1 And they set forward from Elim, and all the multitude of the children of Israel came into the desert of Sin, which is between Elim and Sinai: the fifteenth day of the second month, after they came out of the land of Egypt.
Dukan taron Isra’ila suka tashi daga Elim suka zo hamadar Sin, wadda take tsakanin Elim da Sinai, a rana ta goma sha biyar ga wata biyu, bayan sun fito daga Masar.
2 And all the congregation of the children of Israel murmured against Moses and Aaron in the wilderness.
A hamadan, dukan taro suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna.
3 And the children of Israel said to them: Would to God we had died by the hand of the Lord in the land of Egypt, when we sat over the flesh pots, and ate bread to the full. Why have you brought us into this desert, that you might destroy all the multitude with famine?
Isra’ilawa suka ce musu, “Da ma a hannun Ubangiji ne muka mutu a Masar, inda muka zauna kewaye da tukwanen nama, muna cin duk abincin da muke so, amma kun kawo mu cikin wannan hamada don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.”
4 And the Lord said to Moses: Behold I will rain bread from heaven for you: let the people go forth, and gather what is sufficient for every day: that I may prove them whether they will walk in my law, or not.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan zubo muku burodi kamar ruwa daga sama. Mutanen za su fita kowace rana su tattara abin da zai ishe su na ranan. Ta haka zan gwada su in ga ko za su bi umarnaina.
5 But the sixth day let them provide for to bring in: and let it be double to that they were wont to gather every day.
A rana ta shida za su shirya abin da suka kwaso, wannan kuwa zai zama ninki biyu na abin da sukan tattara na sauran ranaku.”
6 And Moses and Aaron said to the children of Israel: In the evening you shall know that the Lord hath brought you forth out of the land of Egypt:
Saboda haka Musa da Haruna suka ce wa dukan Isra’ila, “Da yamma za ku sani Ubangiji ne ya fitar da ku daga Masar.
7 And in the morning you shall see the glory of the Lord: for he hath heard your murmuring against the Lord: but as for us, what are we, that you mutter against us?
Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, saboda ya ji gunaguninku a kansa. Wane mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?”
8 And Moses said: In the evening the Lord will give you flesh to eat, and in the morning bread to the full: for he hath heard your murmurings, with which you have murmured against him, for what are we? your murmuring is not against us, but against the Lord.
Musa ya kuma ce, “Za ku san cewa shi ne Ubangiji, sa’ad da ya ba ku nama ku ci da yamma, da kuma duk burodin da kuke so da safe, saboda ya ji gunagunin da kuka yi a kansa. Namu a wane? Ai, gunaguninku ba a kanmu ba, amma a kan Ubangiji ne.”
9 Moses also said to Aaron: Say to the whole congregation of the children of Israel: Come before the Lord: for he hath heard your murmuring.
Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka faɗa wa dukan taron Isra’ila, ‘Ku zo gaban Ubangiji, gama ya ji gunaguninku.’”
10 And when Aaron spoke to all the assembly of the children of Israel, they looked towards the wilderness: and behold the glory of the Lord appeared in a cloud.
Yayinda Haruna yake magana da dukan taron Isra’ila, sai suka duba wajen hamada, sai ga ɗaukakar Ubangiji tana bayyana a girgije.
11 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
12 I have heard the murmuring of the children of Israel: say to them: In the evening you shall eat flesh, and in the morning you shall have your fill of bread: and you shall know that I am the Lord your God.
“Na ji gunagunin Isra’ilawa. Ka faɗa musu, ‘A tsakanin fāɗuwar rana da almuru, za ku ci nama, da safe kuma za ku ƙoshi da burodi. Sa’an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku.’”
13 So it came to pass in the evening, that quails coming up, covered the camp: and in the morning, a dew lay round about the camp.
Da yamman wannan rana, sai makware suka rufe dukan sansani, da safe kuma sai ga raɓa ta kewaye sansani.
14 And when it had covered the face of the earth, it appeared in the wilderness small, and as it were beaten with a pestle, like unto the hoar frost on the ground.
Lokacin da raɓar ta watse, sai ga wani abu kamar tsaki, falle-falle kuma da laushi, fari, kamar hazo, a ƙasa.
15 And when the children of Israel saw it, they said one to another: Manhu! which signifieth: What is this! for they knew not what it was. And Moses said to them: This is the bread, which the Lord hath given you to eat.
Sa’ad da Isra’ilawa suka ga wannan, sai suka ce wa junansu, “Mene ne wannan?” Gama ba su san ko mene ne ba. Musa ya ce musu, “Wannan shi ne burodin da Ubangiji ya ba ku ku ci.
16 This is the word, that the Lord hath commanded: Let every one gather of it as much as is enough to eat: a gomor for every man, according to the number of your souls that dwell in a tent, so shall you take of it.
Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Kowane mutum zai tattara bisa ga bukatarsa. Ku tara rabin gallon don mutum guda da yake cikin tentinku.’”
17 And the children of Israel did so: and they gathered, one more, another less.
Isra’ilawa suka yi kamar yadda aka faɗa musu, waɗansu suka tattara da yawa, waɗansu kuma kaɗan.
18 And they measured by the measure of a gomor: neither had he more that had gathered more: nor did he find less that had provided less: but every one had gathered, according to what they were able to eat.
Da suka gwada a mudu, wanda ya tattara da yawa bai sami mafi yawa ba, wanda kuma ya tattara kaɗan bai sami ƙanƙani ba. Kowane mutum ya tattara daidai bukatarsa.
19 And Moses said to them: Let no man leave thereof till the morning.
Sa’an nan Musa ya ce musu, “Kada wani yă bar saura har safe.”
20 And they hearkened not to him, but some of them left until the morning, and it began to be full of worms, an it putrified, and Moses was angry with them.
Duk da haka waɗansu ba su kula da umarnin Musa ba, suka bar saura har safe, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su.
21 Now every one of them gathered in the morning, as much as might suffice to eat: and after the sun grew hot, it melted.
Kowace safiya, kowanne mutum yakan tattara daidai bukatarsa, lokacin da rana ta yi zafi, sai ta narke.
22 But on the sixth day they gathered twice as much, that is, two gomors every man: and all the rulers of the multitude came, and told Moses.
A rana ta shida, suka tattara ninki biyu, mudu biyu ga mutum guda, sai shugabannin taron suka zo suka kawo ƙara wurin Musa.
23 And he said to them: This is what the Lord hath spoken: Tomorrow is the rest of the sabbath sanctified to the Lord. Whatsoever work is to be done, do it: and the meats that are to be dressed, dress them: and whatsoever shall remain, lay it up until the morning.
Shi kuma ya ce musu, “Wannan shi ne umarnin Ubangiji, ‘Gobe za tă zama ranar hutu, Asabbaci mai tsarki ga Ubangiji. Domin haka sai ku toya abin da kuke so ku toya, ku kuma dafa abin da kuke so ku dafa. Abin da ya rage ku ajiye har safe.’”
24 And they did so as Moses had commanded, and it did not putrify, neither was there worm found in it.
Sai suka bar saura har safe, kamar yadda Musa ya umarta, bai kuwa yi wari ko yă yi tsutsa ba.
25 And Moses said: Eat it today, because it is the sabbath of the Lord: today it shall not be found in the field.
Musa ya ce, “Ku ci shi yau, saboda yau Asabbaci ne na Ubangiji. Ba za ku same shi a ƙasa a yau ba.
26 Gather it six days: but on the seventh day is the sabbath of the Lord, therefore it shall not be found.
Kwana shida za ku tattara shi, amma a rana ta bakwai, Asabbaci, ba za a same shi ba.”
27 And the seventh day came: and some of the people going forth to gather, found none.
Duk da haka waɗansu mutane suka fita a ranar Asabbaci don su tattara, amma ba su sami kome ba.
28 And the Lord said to Moses: How long will you refuse to keep my commandments, and my law?
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe za ku ƙi bin dokokina da umarnaina?
29 See that the Lord hath given you the sabbath, and for this reason on the sixth day he giveth you a double provision: let each man stay at home, and let none go forth out of his place the seventh day.
Ku lura fa, ai, Ubangiji ne ya ba ku Asabbaci; shi ya sa a kan ba ku burodi na kwana biyu, a rana ta shida. Kowa ya kamata yă kasance inda yake a rana ta bakwai; kada kowa yă fita.”
30 And the people kept the sabbath on the seventh day.
Sai mutanen suka huta a rana ta bakwai.
31 And the house of Israel called the name thereof Manna: and it was like coriander seed white, and the taste thereof like to flour with honey.
Mutanen Isra’ila suka kira burodin Manna. Manna yana nan fari kamar farin riɗi, ɗanɗanonsa kuma yana kama da masa da aka yi da zuma.
32 And Moses said: This is the word, which the Lord hath commanded: Fill a gomor of it, and let it be kept unto generations to come hereafter, that they may know the bread, wherewith I fed you in the wilderness, when you were brought forth out of the land of Egypt.
Musa ya ce, “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Ku auna mudu guda na Manna, a adana ta dukan zamananku, domin kowane zamani yă ga irin abincin da na ba ku ku ci a hamada, yayinda na fitar da ku daga Masar.’”
33 And Moses said to Aaron: Take a vessel, and put manna into it, as much as a gomor can hold: and lay it up before the Lord to keep unto your generations,
Saboda haka Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki tulu, ka sa mudu guda na Manna a ciki. Sa’an nan ka sa shi a gaban Ubangiji, don a adana don tsararraki masu zuwa.”
34 As the Lord commanded Moses. And Aaron put it in the tabernacle to be kept.
Sai Haruna ya ajiye Mannar a gaban Akwatin Alkawari, don a adana ta kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
35 And the children of Israel ate manna forty years, till they came to a habitable land: with this meat were they fed, until they reached the borders of the land of Chanaan.
Isra’ilawa suka yi shekaru arba’in suna cin Manna, har sai da suka shiga cikin ƙasar da take da mutane, suka ci Manna har zuwa kan iyakar ƙasar Kan’ana.
36 Now a gomor is the tenth part of an ephi.
(Omer guda, daidai ne da kashi ɗaya bisa goma na Efa.)

< Exodus 16 >