< Deuteronomy 3 >

1 Then we turned and went by the way of Basan: and Og the king of Basan came out to meet us with his people to fight in Edrai.
Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
2 And the Lord said to me: Fear him not: because he is delivered into thy hand, with all his people and his land: and thou shalt do to him as thou hast done to Sehon king of the Amorrhites, that dwelt in Hesebon.
Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
3 So the Lord our God delivered into our hands, Og also the king of Basan, and all his people: and we utterly destroyed them,
Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
4 Wasting all his cities at one time, there was not a town that escaped us: sixty cities, all the country of Argob the kingdom of Og in Basan.
A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
5 All the cities were fenced with very high walls, and with gates and bars, besides innumerable towns that had no walls.
Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
6 And we utterly destroyed them, as we had done to Sehon the king of Hesebon, destroying every city, men and women and children:
Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
7 But the cattle and the spoils of the cities we took for our prey.
Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
8 And we took at that time the land out of the hand of the two kings of the Amorrhites, that were beyond the Jordan: from the torrent Amen unto the mount Hermon,
A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
9 Which the Sidonians call Sarion, and the Amorrhites Sanir:
(Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
10 All the cities that are situate in the plain, and all the land of Galaad and Basan as far as Selcha and Edrai, cities of the kingdom of Og in Basan.
Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
11 For only Og king of Basan remained of the race of the giants. His bed of iron is shewn, which is in Rabbath of the children of Ammon, being nine cubits long, and four broad after the measure of the cubit of a man’s hand.
(Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
12 And we possessed the land at that time from Aroer, which is upon the bank of the torrent Amen, unto the half of mount Galaad: and I gave the cities thereof to Ruben and Gad.
Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
13 And I delivered the other part of Galaad, and all Basan the kingdom of Og to the half tribe of Manasses, all the country of Argob: and all Basan is called the Land of giants.
Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
14 Jair the son of Manasses possessed all the country of Argob unto the borders of Gessuri, and Machati. And he called Basan by his own name, Havoth Jair, that is to say, the towns of Jair, until this present day.
Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
15 To Machir also I gave Galaad.
Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
16 And to the tribes of Ruben and Gad I gave of the land of Galaad as far as the torrent Amen, half the torrent, and the confines even unto the torrent Jeboc, which is the border of the children of Ammon:
Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
17 And the plain of the wilderness, and the Jordan, and the borders of Cenereth unto the sea of the desert, which is the most salt sea, to the foot of mount Phasga eastward.
Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
18 And I commanded you at that time, saying: The Lord your God giveth you this land for an inheritance, go ye well appointed before your brethren the children of Israel, all the strong men of you,
Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
19 Leaving your wives and children and cattle. For I know you have much cattle, and they must remain in the cities, which I have delivered to you.
Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
20 Until the Lord give rest to your brethren, as he hath given to you: and they also possess the land, which he will give them beyond the Jordan: then shall every man return to his possession, which I have given you.
sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
21 I commanded Josue also at that time, saying: Thy eyes have seen what the Lord your God hath done to these two kings: so will he do to all the kingdoms to which thou shalt pass.
A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
22 Fear them not: for the Lord your God will fight for you.
Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
23 And I besought the Lord at that time, saying:
A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
24 Lord God, thou hast begun to shew unto thy servant thy greatness, and most mighty hand, for there is no other God either in heaven or earth, that is able to do thy works, or to be compared to thy strength.
“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
25 I will pass over therefore, and will see this excellent land beyond the Jordan, and this goodly mountain, and Libanus.
Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
26 And the Lord was angry with me on your account and heard me not, but said to me: It is enough: speak no more to me of this matter.
Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
27 Go up to the top of Phasga, and cast thy eyes round about to the west, and to the north, and to the south, and to the east, and behold it, for thou shalt not pass this Jordan.
Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
28 Command Josue, and encourage and strengthen him: for he shall go before this people, and shall divide unto them the land which thou shalt see.
Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
29 And we abode in the valley over against the temple of Phogor.
Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.

< Deuteronomy 3 >